Connect with us

Labarai

Manyan Sanatoci sun kai wa Tinubu ziyara bayan dakatar da Sanata Ningi

Published

on

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya shiga bayan labule da jagororin Majalisar Dattawa a Yammacin wannan Talatar.

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio ne ya jagoranci tawagar sanatocin da ta kai wa shugaban ƙasar ziyara kamar yadda Aminiya ta ruwaito.

Ganawar dai na zuwa ne sa’o’i bayan da Majalisar Dattawan ta dakatar da Sanatan Bauchi ta Tsakiya, Abdul Ahmed Ningi har na tsawon watanni uku kan sukar da ya yi dangane da Kasafin Kuɗin ƙasar na bana.

Cikin tawagar sanatocin da ta ziyarci Fadar Shugaban Ƙasar har da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin.

KU KUMA KARANTA: Majalisa ta dakatar da sanata Abdul Ningi na tsawon watanni uku

Neptune Hausa ta ruwaito cewa, Sanata Ningi wanda shi ne Shugaban Ƙungiyar Sanatocin Arewa kuma Shugaban Kwamitin Kidayar Al’umma na Majalisar Dattawa, ya yi murabus daga duk muƙaman bayan hukuncin da aka ɗauka a kansa.

An dai dakatar da Sanata Abdul Ningi a ranar Talata, bisa zargin da ya yi na cewa an yi cushe naira tiriliyan 3.7 a Kasafin Kuɗin 2024.

Dakatar da Sanatan na zuwa ne bayan da aka yi wani zama da aka yamutsa hazo a zauren majalisar.

Wani mamba a kwamitin Kasafin Kuɗi a Majalisar Dattawa, Jimoh Ibrahim ne ya fara gabatar da ƙudirin dakatar da Sanata Ningi na tsawon wata 12, bisa zarginsa da ba da bayanai ba daidai ba waɗanda suke daidai da aikata babban laifi, da kuma hargitsa zaman lafiya a Majalisar Dokoki da ma ƙasar baki ɗaya.

Wasu ‘yan majalisar kamar Sanata Asuquo Ekpenyong sun goyi bayan ƙudirin Ibrahim ɗin.

Amma Ekpenyong, ɗan majalisa mai wakiltar Kuros Riba ta Kudu da kuma Sanata Abdulfatai Buhari daga Oyo ta Arewa, sun roƙi a rage tsawon dakatarwar zuwa wata shida da uku.

Akpabio, wanda ya bayyana laifukan Ningi a matsayin ‘manya’, ya gudanar da wata ƙuri’a da baki inda mafi yawan ’yan majalisar suka amsa amincewa da dakatar da Ningi na tsawon wata uku.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like