No menu items!

Sample Page Title

Date:

Malaman firamare sun tsunduma yajin aikin sai-baba-ta-gani a Abuja

Malaman da ke koyarwa a makarantun firamare na gwamnati a birnin tarayya Abuja sun tsunduma yajin aikin sai baba-ta-gani.

Hakan na zuwa ne, bayan wa’adin kwanaki 14 da ƙungiyar malaman ta bayar ga ƙananan hukumomi 6 na birnin ya cika kuma ba a biya musu buƙatunsu ba.

Daily Trust ta ruwaito cewa ɗalibai da su ka je makaranta a yau Laraba sun dawo gida inda suka ce malaman su sun koro su a yayin da su ka isa ƙofar shiga makarantar.

Da ya ke tabbatar da lamarin, shugaban Kungiyar Malamai ta Kasa ,NUT, da ke Kubwa, Comrade Ameh Baba, ya ce an zauna tare da cimma matsaya kafin shiga yajin aikin.

KU KUMA KARANTA:Za mu kammala aikin layin dogo daga Ibadan-Abuja-Kaduna-Kano ba da jimawa ba – Gwamnatin tarayya

Ya ce sun dauki matakin shiga yajin aikin ne don tilastawa kananan hukumomin shida wajen cika alkawarin da suka dauka na biyan ariyas kaso 60 da suka rike.

Comrade Ameh ya yi Alla-wadai ga kananan hukumomin kan kin biyan alawus na kaso 40 ga Malaman da kuma kin karin albashi na kaso 25 da 35 ga Malaman.

Ya ce kasancewar ilim firamare shi ne tushe kamata yayi a bashi dukkan goyan baya da kulawa.

Kungiyar tayi gargadin cewa yajin aikin, yanzu ta fara.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...