Connect with us

Kasashen Waje

Makauniyar masaƙiya na ɗaukar nauyin iyalinta da sana’ar saƙa tabarma

Published

on

Cikin ƙwaryar Dar es Salaam, birni mafi girma a Tanzania, akwai yankin Chamazi inda Barati John take saƙa tabarma ta samu kuɗin ɗaukar nauyin kanta da ƴaƴanta huɗu.

Bahati John wacce aka fi sani da Mrs Khadija, ta gwanance ƙwarai wajen saƙa tabarma, ta irin baiwar da Allah ya yi mata, ta iya sarrafa abu da hannu, bayan ƙawayenta sun koya mata sana’ar tun shekarar 1994.

Ta gaya wa TRT Afrika cewa ta soma sha’awar saƙa ne tun tana ƙarama.

Wata rana, da ta gaya wa wata ƙawarta cewa tana sha’awar saƙa, sai ƙawar ta soma koya mata ta hanyar riƙe hannayenta sannan tana kwatanta mata yadda ake yi.

Bahati ta ce “Ƙawata ta fara koya min ta hanyar riƙe hannayena, saboda makafi suna aikinsu ne ta hanyar taɓa abu.”

“Ta gaya mini na saƙa kamar haka, wannan shi ne yadda mutane suke saƙa.”

Ƙasar da ke yankin Afrika ta Gabas tana fama da matsin tattalin arziki kama matasa sun bayyana damuwarsu game da rashin aikin yi. Amma Bahati ba ta taɓa ƙyale nakasarta ta kawo mata tarnaƙi wajen neman na kanta ba.

Sana’ar ta dogara ne da amfani da kaba kuma tana tsimin kuɗi daga cikin kuɗin da mahaifiyarta ta tanada don hidimar gida, ta sayi kayan aikin saƙa tabarmu.

KU KUMA KARANTA: Abun sha’awa: Yaro mai fuskar al’ajabi da shuɗin launin idanu

Bahati ta gaya wa TRT Afrika cewa ya danganci girman tabarmar, tana ɗaukar tsakanin makonni uku zuwa wata ɗaya ta gama saƙa tabarma ɗaya.

Uwar ƴaƴa guda huɗun ta ce har yanzu tana da ƴaƴa guda biyu masu zuwa makaranta waɗanda take ɗaukar nauyin da sana’ar tata.

“Idan na sayar da tabarmata, ina magance matsalolin da ƴaƴana ke fuskanta ne,” in ji Bahati.

Bahati ta bayyana wa maƙwabta ƙarara cewa, ba ta son a dinga tausaya mata saboda nakasarta.

Da sanyin safiya a kullum, tana barin gidanta ta tafi wajen aiki kamar kowa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kasashen Waje

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

Published

on

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Amurka ta yi Allah wadai da kalaman nuna wariyar launin fata ga ‘yan wasanta a ranar Alhamis, bayan da Panama ta yi nasara a kan Amurka da ci 2-1 a gasar cin kofin Copa America.

A wani saƙo da ta wallafa a shafin X, hukumar ƙwallon ƙafa ta Amurka ta ce “Babu shakka, babu wuri a cikin wasa na irin wannan halayya ta nuna ƙiyayya da wariya.”

Sanarwar ta ƙara da cewa “Waɗannan ayyukan ba kawai ba za’a amince da su ba ne, amma kuma sun saɓa wa kimar mutuntawa da haɗa kai da muka ɗauka a matsayin hukuma.”

KU KUMA KARANTA:Manchester City ta lashe Firimiyar Ingila sau huɗu a jere

Timothy Weah, wanda baƙar fata ne, yana ɗaya daga cikin ‘yan wasan da aka ci zarafin su. An bai wa ɗan wasan gaba na Amurka jan kati kai tsaye a minti na 18 da fara wasa, saboda hannu da ya sa ya bugi ɗan wasan Panama a bayan kan sa a lokacin da ƙwallon ta fita wajen filin wasa.

Ɗan wasan Amurka Folarin Balogun ya zura ƙwallo a minti na 22 da fara wasan bayan an bai wa Weah jan kati kafin ɗan wasan Panama Blackman ya farke a minti na 26.

Fajardo ya zura ƙwallo da ta bai wa Panama nasara da ci 2-1 a minti na 83.

Weah ya fitar da wata sanarwa ta kafafan sada zumunta, inda ya bayar da haƙuri tare da neman gafarar waɗanda ya ɓata wa rai.

Yanzu haka dai Amurka, wacce ita ce ke karɓar baƙuncin gasar cin kofin na Copa America, muddin tana son zuwa zagaye na gaba to dole ne ta yi nasara a wasanta da Uruguay da zura ƙwallaye wanda ko da Panama ta yi nasara kan Bolivia za ta samu tsallake wa.

Continue Reading

Kasashen Waje

An tafka muhawarar farko tsakanin shugaba Biden da Trump

Published

on

An tafka muhawarar farko tsakanin shugaba Biden da Trump

An tafka muhawarar farko tsakanin shugaba Biden da Trump

Shugaban Amurka Joe Biden da tsohon shugaban ƙasar Donald Trump sun gwabza muhawara a daren Alhamis, inda suka fafata kan tattalin arziƙin Amurka da harkokin ƙasashen waje da haƙƙin zubar da ciki da kuma batun ƙaura daga kan iyakar Mexico zuwa Amurka.

“Muna tamkar a wata matalauciyar ƙasa a duniya kuma abin kunya ne,” in ji Trump ya faɗa yayin muhawarar da aka watsa ta talabijin ga ƙasa baki ɗaya, daga hedkwatar gidan talabijin na CNN da ke Atlanta.

“Ba a mutunta mu,” in ji Trump, yana zargin Biden. “Suna tunanin mu wawaye ne.”

Biden ya mayar da martani lokaci guda, yana kallon Trump. Tare da cewa “Wannan shi ne shugaban ƙasa mafi muni a tarihin Amurka. Wannan mutumin bai san ma’anar dimokuraɗiyyar Amurka ba.”

Haɗuwar Biden-Trump, watanni huɗu gabanin zaɓen ranar 5 ga watan Nuwamba, ita ce muhawara ta farko da aka taɓa yi a zagaye na huɗu na zaɓen shugaban ƙasar Amurka.

Hakanan sake haɗuwa ne tun muhawarar su guda biyu a shekarar 2020, wanda ya faru a cikin watanni biyu kafin Biden ya kayar da yunƙurin sake zaben Trump na wa’adi na biyu a Fadar White House.

Muhawarar ta ranar Alhamis ita ce karo na farko da shugabannin Amurka biyu suka taɓa yin muhawara a tsakaninsu, kuma shi ne karo na farko, da Biden da Trump suka haɗu a ɗaki ɗaya tun bayan muhawarar da suka yi a watan Oktoban 2020.

KU KUMA KARANTA:Biden ya yi alƙawarin kare Isra’ila daga harin ramuwar gayya na Iran

Trump ya tsallake bikin rantsar da Biden a watan Janairun 2021, kuma tun daga lokacin suka yi ta zage-zage da juna, ciki har da matakin muhawara a daren Alhamis.

A cikin ‘yan kwanakin nan, Trump ya yi ba a game da shirye-shiryen muhawarar Biden, inda ya ba da shawarar cewa zai bukaci ƙarin ƙarfi daga likita don samun damar iya muhawarar ta mintuna 90, gaba da gaba.

Trump ya faɗa wa wani gangamin magoya baya a Philadelphia cewa, “A yanzu haka, Joe ya tafi gidan katako don yin nazari,” yayin da yake zayyana alamomi da hannunsa. “Yanzu yana barci, saboda suna son ya samu ƙarfi.”

Continue Reading

Kasashen Waje

Kotun duniya ta umurci Isra’ila ta dakatar da kai farmaki a Rafah

Published

on

Kotun duniya ta umurci Isra’ila ta dakatar da kai farmaki a Rafah

A ranar Juma’a ne babban kotun duniya ICJ ta umarci Isra’ila da ta dakatar da hare-haren da take yi a Rafah, birnin da ke kudancin Gaza inda Falasɗinawa sama da miliyan ɗaya suka nemi mafaka a cikin mawuyacin hali.

Ko da yake da wuya Isra’ila ta bi wannan umarni, wanda babbar kotun Majalisar Ɗinkin Duniya ba ta da hurumin aiwatar da shi, amma hukuncin da aka yanke zai ƙara matsin lamba kan ƙasar.

A ci gaba da ƙalubalantar ɓacin ran da ƙasashen duniya suka yi kan rikicin jin kai a yankin, sojojin Isra’ila sun ci gaba da kai munanan hare-haren da suka ƙaddamar sakamakon hare-haren Hamas na ranar 7 ga watan Oktoba.

KU KUMA KARANTA:Babbar Kotun MƊD ta fara sauraron ƙara kan afka wa Rafah da Isra’ila ta yi

Tattaunawar tsagaita buɗe wuta ta ci tura, duk da matsin lamba da ake yi a gida na firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu na ganin an sako mutanen da a ka yi garkuwa da su a Gaza.

Umurnin na ICJ ya biyo bayan roƙon gaggawa da ƙasar Afirka ta Kudu ta gabatar a wani ɓangare na shari’ar da take ci gaba da yi a kotun da ke birnin Hague na ƙasar Netherlands, inda ta zargi Isra’ila da aikata kisan kiyashi a hare-haren da ta shafe watanni ana kai wa Gaza, zargin da Isra’ila da Amurka suka musanta.

Mai yiyuwa ne shari’ar za ta ɗauki shekaru ana warwarewa, amma Afirka ta Kudu ta nemi umarnin wucin gadi don kare Falasɗinawa.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like