Connect with us

Laifi

Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus

Published

on

A ci gaba da matsalolin tsaro da ke addabar al’ummar jihar Anambara, rahotanni na cewa wasu ‘yan bindiga sun sake gudanar da mugun aiki a gidan wani Basarake a jihar.

Wasu mutane da ake zargin ‘yan bindiga ne sun bankawa gidan mai sarautar gargajiya wuta a jihar Anambra.

Mai sarautar gargajiyar a ƙauyen Isseke da ke ƙaramar hukumar Ihiala da ke jihar, Igwe Emmanuel Nnabuife ya tabbatar da lamarin.

Wannan na zuwa mako ɗaya bayan ‘yan bindiga sun sace direban tsohon gwamnan jihar, Chinwoke Mbadinuju, cewar Premium Times.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga a Sakkwato sun ƙona wata mata da ‘ya’yanta biyu da kuma surukanta har lahira

Lamarin ya faru ne yayin da ya ke gudanar da bikin binne ɗan uwansa da ya rasu a ƙauyen Isseke.

Rahotanni sun tabbatar cewa direban ya gagara biyansu kuɗaɗen su kafin binne ɗan uwan nasa inda suka farmaki gidansa da dare.

Maharan sun durfafi gidan nasa inda suka ta harbi a sararin samaniya yayin da suka ɗauke shi zuwa wani da ba a sani ba.

Yayin da ya ke tabbatar da faruwar lamarin, Igwe Emmanuel Nnabuife ya ce maharan sun ƙona masa gidansa ƙurmus.

Ya koka kan yadda aka kai masa farmakin inda ya ce ba shi da matsala da kowa a yankin da za a yi masa haka, cewar Tori News.

Ya ce:“Da gaske ne an ƙona mini gida kurmus wanda a yanzu haka na rasa komai da na sha wahalar nema a rayuwa, yanzu ba ni da gida.

“Komai ya ƙone amma nagode wa Allah babu rasa rai yayin lamarin da ya faru wanda ya tayar min da hankali.”

Kwamishinan ‘yan sanda a jihar, Aderemi Adeoye ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce yanzu haka an fara bincike.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda

Published

on

Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda

Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda

Daga Ibraheem El-Tafseer

Aƙalla mutane shida ne suka mutu inda wasu 15 suka jikkata a wani harin ƙunar baƙin wake da aka kai a garin Gwoza na jihar Borno.

Wani abin takaici ya faru ne a lokacin da ‘yar ƙunar baƙin wake ta tayar da bam a garin Gwoza, ranar Asabar.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, (NAN), ya ruwaito cewa an kai harin ne a wani wurin shaƙatawa na motoci da ake ƙira Marrarraban Gwoza.

Kwamishinan ‘yansandan jihar Borno Yusuf Lawal ya tabbatar da faruwar harin yana mai cewa wata ‘yar ƙunar baƙin wake ce ta kai harin.

Lawal ya ce jami’in ‘yansandan shiyyar Gwoza ne ya sanar da shi cewa aƙalla mutane shida ne suka mutu inda aka kwashe wasu 15 zuwa asibiti.

Wani ganau mai suna Buba, ya shaida wa NAN cewa ‘yar ƙunar baƙin waken ta nufi tsakiyar wani bikin aure ne, inda ta tayar da bam ɗin a nan.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Buba ya ce harin ya rusa farin ciki da murnar wannan rana ta musamman, inda ya bar iyalai da ‘yan uwa cikin makoki.

Wani wanda ya shaida lamarin, Muhammed Kasim, ya ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 1:30 na rana.

“Mun ji ƙarar fashewar abubuwa, tare da ƙura, sai muka ga gawarwaki a ƙasa.”

Ya ce an kwashe da dama daga cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su zuwa asibiti yayin da aka tura jami’an tsaro domin dawo da zaman lafiya a yankin. (NAN).

Continue Reading

Laifi

’Yan sanda sun kama wani matashi kan zargin satar kuɗi ta na’urar ATM

Published

on

’Yan sanda sun kama wani matashi kan zargin satar kuɗi ta na’urar ATM

’Yan sanda sun kama wani matashi kan zargin satar kuɗi ta na’urar ATM

Daga Muhammad Kukuri

Rundunar ’yan sandan jihar Gombe ta kama matashin, wanda ake wa inkiya da Mai Shanawa ne kan zargin aikata yaudara da satar kuɗi da katin ATM ta na’urar PoS.

Matashin ya faɗa komar ’yan sanda ne bayan wani mazaunin garin Abuja Bula, da ke Karamar Hukumar Kwami ya kai rahoto ofishin ’yan sanda na Dukku a ranar 22 ga Watan Mayu 2024.

Muhammad yana zargin matsahin da yaudarar sa da kuma satar kudi a asusun bankinsa a banki a lokacin da yaje cire kuɗi da katinsa na ATM.

Ya ce bayan ya saka katinsa  na’urar ATM ba ta ba shi kudin ba, ashe matashin yana biye da shi a baya, sai ya yaudare shi cewa ya shiga cikin banki ya yi musu bayani.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sandan Najeriya sun kama waɗanda ake zargi da satar mutane a titin Abuja-Kaduna

Bai ankara ba, ashe a lokacin matashin ya zare masa katin ya bar shi a wajen.

Mutumin ya ci gaba da cewa, yana tsaye yana jira can sai yaga sako an cire Naira dubu ɗari uku daga asusunsa ta wani POS da ke kusa da bankin a garin na Dukku.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, ASP Buhari Abdullahi, ya ce bayan  samun rahoton ƙorafin suka shiga bincike suka yi sa’ar kama wanda ake zargin.

ASP Buhari Abdullahi ya ce a yayin binciken sun samu katunan cire kuɗi na ATM daban-daban har guda 21, ciki harda na wanda ya kai ƙorafin, a hannun matashin.

Sannan ya ce suna kan ci gaba da bincike, da zarar sun kammala za su tura wanda ake zargin zuwa kotu.

Continue Reading

Laifi

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Published

on

'Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaki Rarara

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Daga Idris Umar, Zariya

Labarin dake zuwa mana yanzu shine ’yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar shahararren mawaƙin siyasa, Dauda Kahutu Rarara.

Kamar yadda akace an yi garkuwa da Hajiya Hakima Adamu ne a gidanta da yankin Kahutu a ƙaramar hukumar Ɗanja ta jihar Katsina, kamar yadda aka tseguntawa manema labarai

Wasu mutane a ƙauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi gaba da ita.

“A kafa suka zo, kuma kasancewar ba su yi harbi ba a lokacin da suka kai harin suka yi garkuwa da ita cikin ’yan mitoci. Dattijuwar ba ta yi musu turjiya ba a lokacin da suka ce ta biyo su.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai da dama a jihar Delta

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka suka tafi da ita.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda suna dauke da bindigogi,” in ji wani mazaunin kauyen na Kahutu, kamar yadda majiyarmu ta jiyo.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like