No menu items!

Sample Page Title

Date:

Magoya bayana su zaɓi jam’iyar ADC a zaɓukan cike-gurbi – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban Najeriya a Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi ya yi ƙira ga masu kaɗa ƙuri’a a Najeriya, musamman masoyansa na ƙungiyar Obidient da su zaɓi jam’iyyar ADC ne a zaɓukan cike gurbi da za a yi a ranar Asabar (16 Agusta).

Obi ya bayyana haka ne a shafinsa na Facebook, inda ya ce, “a game da zaɓukan da za a yi a gobe Asabar, 16 ga watan 2025 domin cike gurbin wasu kujeru a jihohi 16 na Najeriya, tunda jam’iyyar LP ba ta da ƴantakara saboda kotu ta hana sanadiyyar rikice-rikicen da ke cikin jam’iyyar, ina kira ga masoyana da su su zaɓi jam’iyyar haɗaka ta ADC a jihohinsu.”

KU KUMA KARANTA: Zan yi haɗaka da sabuwar jam’iyyar ADC don a kayar da Tinubu, amma ba zan fice daga jam’iyar PDP ba – Sule Lamiɗo

Wannan jawabin na Obi na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta muhawara game da yunƙurin haɗakar siyasa, inda ake tunanin manyan jam’iyyun hamayya za su iya haɗuwa a guri ɗaya domin fuskantar Tinubu a zaɓe mai zuwa.

Za a zaɓen ne a jihohi 16 a Najeriya, inda za a yi zaɓen cike gurbi na sanatoci biyu, da majalisar wakilai biyar da majalisar jiha guda 9 a jihohi daban-daban.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...