Ma’aitakan filayen jiragen sama na yajin aiki a Najeriya

0
218

Ƙungiyar Ma’aikatan filayen jiragen sama ta Najeriya sun rufe filin jirgin sama na Malam Aminua Kano da ke kano sakamakon yajin aikin da uwar ƙungiyar ta ƙasa ta fara gudanarwa a yau.

 Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito cewa an soke tashin wasu jiragen da aka tsara tashinsu daga filin jirgin da safiyara yau Litinin.

Wani jami’in Filin jirgin ya ce an soke tashin jirgin AZMAN zuwa Abuja da na Max Air zuwa Legas, bayan da fasinjoji suka riga suka shiga jiragen.

Yajin aikin na zuwa ne sakamakon saɓani da aka samu tsakanin hukumar kula da filayen jiragen sama ta ƙasar da hukumar kula da sararin samaniya ta ƙasar kan wasu batutuwa.

Leave a Reply