No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ma’aikatan lafiya na Najeriya sun janye yajin aikinsu na kwanaki 12 bayan wata ganawa da suka yi da shugaban ƙasar, Bola Ahmed Tinubu a ranar Litinin.

Ƙungiyar ma’aikatan ta JOHESU, wadda ta yi ganawar da shugaba Tinubu, ta ce ta yanke shawarar janye yajin aikin ne domin bai wa gwamnati wa’adin mako uku domin shawo kan matsalolin da suke fuskanta.

Mataimakin shugaban ƙungiyar na ƙasa, Dakta Obinna Ogbonna ya ce “an samu ci gaba” a tattaunawar da suka yi da shugaban ƙasa.

“Amincewa tamkar abu ne mai haɗari, amma tun da a yanzu muna magana ne da sabon shugaban ƙasa, wanda da kansa ya roƙi mu ba shi lokaci, ya kamata mu ba shi.

KU KUMA KARANTA: Ƙungiyar ma’aikatan wutar lantarki ta Najeriya za ta shiga yajin aiki

“Bayan kwanakin 21 za mu duba inda ake sannan mu ɗauki mataki na gaba.” in ji Dakta Obinna a tattaunawarsa da BBC.

Ma’aikatan lafiyar dai na nema ne a yi watsi da tsarin biyan albashi na bai-ɗaya, da biyansu alawus-alawus ɗin aiki, da sake duba shekarun yin ritaya da dai sauran su.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...