Connect with us

Kiwon Lafiya

Likitocin Najeriya sun yi barazanar yajin aiki a Nasarawa

Published

on

Ƙungiyar likitocin Najeriya reshen jihar Nasarawa (NMA), ta baiwa gwamna Abdullahi Sule na jihar wa’adin kwanaki 21 da ya magance matsalolin jin daɗin jama’a da suka shafi membobinsu ko kuma su fuskanci yajin aikin.

Dakta Peter Attah, shugaban NMA a jihar, shi ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai ranar Talata a Lafiya, babban birnin jihar.

Ya bayyana cewa wa’adin zai fara ne a ranar talata 13 ga watan Yuni kuma ya kare a ranar 3 ga watan Yuli.

Ya yi barazanar cewa likitocin za su janye aikinsu idan gwamnati ta ƙasa biya musu buƙatunsu kafin cikar wa’adin.

Ya zayyana wasu daga cikin matsalolin da suka haɗa da rashin aiwatar da ƙarin girma ga Likitoci da ƙarin albashi na shekara sama da shekaru tara, rashin aiwatar da mafi ƙarancin albashi na dubu 30,000 da kuma gyara sakamakon haka.

KU KUMA KARANTA: Ma’aikatan lafiya a Najeriya sun janye yajin aiki

Sauran kuma rashin aiwatar da da’awar bayar da izinin da aka yi bita da kuma bashin albashi na watanni 17, Babban nauyin Haraji da rashin isassun ma’aikata da kuma yawan aiki.

Ya ce likitoci 25 da suka yi aiki a shekarar 2014 a asibitin ƙwararru na Dalhatu Araf da ke DASH da Lafiya da kuma hukumar kula da asibitoci ba a ƙara musu girma ba shekara tara yanzu.

Shugaban NMA ya ƙara da cewa ƙungiyar ta ziyarci gwamnan ne a ranar 17 ga watan Junairu, 2023, inda ta gabatar da batutuwan domin duba lamarin, amma ta yi mamakin dalilin da ya sa ba a yi wani abu ba.

A cewarsa, ƙungiyar ta bai wa gwamnatin jihar isasshen lokaci domin ta magance musu buƙatunsu amma gwamnati ta yi watsi da halin da suke ciki.

Shugaban ya bayyana cewa ƙungiyar ta nuna fahimta da gwamnati wajen tabbatar da daidaiton masana’antu, amma gwamnati ta ka sa mayar da martani.

Dakta Attah ya ci gaba da cewa, Likitoci 27 ne suka bar aikin jihar a cikin wata ɗaya da ya gabata sakamakon rashin jin daɗin rayuwa.

“Likitoci 20 sun yi murabus daga DASH sannan bakwai daga Hukumar Kula da Asibiti a cikin makonni uku da suka gabata,” in ji shi.

Ya bayyana cewa ƙarancin likitocin yana ƙara matsa lamba ga ‘yan tsirarun da suka yanke shawarar zama, ta yadda a yanzu likitocin sun gwammace yin aiki a yankunan karkara fiye da kayan aiki a garin.

Ya ce ma’aunin hukumar lafiya ta duniya shi ne ana sa ran likita ɗaya zai kai kimanin mutane 600, amma rabon da ake samu a jihar Nasarawa likita ɗaya ne ga mutane sama da dubu 20,000.

Dakta Attah ya ba da shawarar cewa, yana da kyau a inganta jin daɗin likitocin don rage zubar da ƙwaƙwalwar fiye da maye gurbinsu saboda har yanzu sabbin za su tafi bayan wani lokaci.

Shugaban NMA ya ba da shawarar a sake duba kuɗaɗen alawus-alawus, na ƙiran waya, rage haraji da kuma rashin biyan alawus-alawus da baiwa likitoci motoci da rancen gidaje a wani mataki na daƙile taɓarɓarewar ƙwaƙwalwa a jihar.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Ƙungiyar likitoci ta janye yajin aikin da ta shiga | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kiwon Lafiya

Gwamnatin tarayya ta hana amfani da sirinjin allura na ƙasashen waje a manyan asibitoci ƙasar

Published

on

Gwamnatin tarayya ta umurci dukkan shugabannin manyan asibitocin gwamnatin tarayya da su sayi allura da su riƙa amfani da allura da da ake ƙera su a gida kuma hukumar NAFDAC ta amince da su.

Sabuwar umarnin na ƙunshe ne a cikin wata takardar ga dukkan shugabannin asibitoci mai ɗauke da sa hannun ƙaramin ministan lafiya, Dakta Tunji Alausa, a yau Juma’a.

Ministan ya ce an ba da wannan umarnin ne domin bunƙasa samar da kayayyakin da ake ƙera wa a cikin gida da kuma kare masana’antun ƙasar daga kwararar kayayyakin ƙasashen waje.

Sanarwar ta kuma umarci hukumar ta NAFDAC ta dakatar da bayar da lasisin shigo da allura da sirinji da aka ƙera daga ƙasashen waje.

Alausa ya ce ɓangaren lafiya ya gano masana’antar har haɗa magunguna ta cikin gida da ke samar da allura da sirinji waɗanda ke cikin matsala matuƙa saboda wannan mummunar harkar.

Ya kuma ce daga cikin kamfanonin har haɗa magunguna guda tara na cikin gida da suke samar da allura da sirinji shekaru takwas da suka gabata, shida sun rufe saboda zubar da kayayyakin da ba su da inganci a kasuwa.

KU KUMA KARANTA:NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

“Shugaban ƙasa ya ba da umarnin cewa dole ne a daina wannan. Dukkanmu mun amince da ɗaukar matakan da suka dace don magance wannan mummunan yanayi cikin gaggawa.

“A bisa haka, hukumar ta NAFDAC ta dakatar da bayar da lasisin shigo da allura da sirinji da aka ƙera daga ƙasashen waje.

“Haka kuma shi ne a soke jerin sunayen kamfanonin da ke da hannu wajen shigo da waɗannan kayayyakin da ke ci gaba,” in ji shi

Continue Reading

Kiwon Lafiya

Amfanin ‘Dental floss’ a haƙora don tsaftace baki

Published

on

Daga Aisha Musa Auyo

Dental floss dai wani zare ne siriri na roba da ake sawa a tsakanin haƙora don cire abincin da ya maƙale a wurin. Wannan abinci da ke maƙale a tsakanin haƙora, brush ba ya fitar da shi. Shi ne yake taruwa ya zama ‘plaque’. Shi plaque ɗin wannan abincin da ya maƙale ne yake taruwa sai ya zama abincin bacteria.

Wannan dattin yana sa baki wari, yana sa haƙora su canza kala. Yana sa haƙora su yi ta ciwo wataran ma har sai an cire haƙorin, domin wannan bacteriar da ke ci daga gareshi tana kashe haƙori.

To shi wannan zaren yana zuwa a nau’i daban-daban, an yi shi ne siriri yadda ze iya shiga tsakanin haƙora yana fito da duk abin da ya maƙale ba tare da an wahala ba ko an ji zafi. Wani yakan zo da ƙamshin minti, vanilla, da sauransu, wani kuma kawai zaren ne babu ƙamshi.

Mafi yawancin ciwon haƙori ko warin baki wannan maƙallen abincin ke kawo shi. Idan mutum ya je Asibitin haƙori, akan yi masa wannan sakace tsakanin duk haƙoransa duka. Wato duk ranar da kuka fara flossing zai sha mamakin abin da zai fito tsakanin haƙoranku.

KU KUMA KARANTA: Sama da mutane miliyan 73 ne ke fama cutar ruɓewar haƙora a Filipin

Wato abin ya bani mamaki da na tambayi mutane ko suna flossing na ga da yawansu ba su ma san mene ne shi ba. Kamata ya yi flossing ya zama normal kamar brush. A ƙa’ida akan so mutum ya yi wannan sakacen tsakanin haƙoran kamar sau biyu a rana, yadda yake brush, amma mutum zai iya yin fiye da haka. In da hali duk lokacin da mutum ya ci abinci ya kamata ya yi flossing.

Akwai mouth wash da kan taimaka wajen fitar da waɗannan maƙallalun abincin, yayin da aka kurkure baki da shi na mintuna. Haka zalika, kurkure baki da ruwan kananfari ma na taimakawa wajen fiddasu. Amma babu abin da ya kai saka wannan zare a tsakanin haƙora ɗaya bayan ɗaya fitar da wannan abu da ke maƙalewa a tsakanin haƙoran.

Dan Allah a guji tsinken sakace, ba ɗaya yake da floss ba. Shi tsinken yana da kauri yana sa a samu rami tsakanin haƙoran da ake yawan sakace wa. Sannan katako ne yakan karye ma, kuma yakan jima mutum rauni.

A taƙaice, yin floss na ƙara wa mutum lafiyar haƙora, kyan haƙora, numfashi mai tsafta, da kuma jin daɗi wajen mua’amala da jamaa. Yin floss na raba mutum da ciwon haƙori, da kuma dauɗar haƙora. Floss na da sauƙin kuɗi sosai, ana iya samunsa a manyan shaguna, ko asbitin haƙori, har ma da wurin masu sayar da robobin abincin biki, domin ana sa shi a cikin packs ɗin abinci.

Dan Allah ka da mu yi wasa da yin floss. Akwai Hadisin da Annabi Muhammad (SAW) ya ce, ba dan ka da ya takurawa al’ummarsa ba, da ya mayar da yin aswaki kafin yin kowacce sallah ya zama wajibi. Wannan yana nuna mana tsantsar amfanin tsaftar baki ko a addini ma.

Continue Reading

Kiwon Lafiya

Cutar sanƙarau ta kashe mutum 85 a Yobe

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Gwamnatin jihar Yobe ta ce cutar sanƙarau ta kashe mutum 85 tsakanin Janairu da Afrilu sakamakon ɓarkewar cutar a jihar.

Kwamishinan lafiya na jihar, Dakta Muhammad Lawan Gana ne ya tabbatar da hakan a wani taron manema labarai a birnin Damaturu.

Ya ƙaryata rahotannin da ake yaɗawa a shafukan sada zumunta da ke cewa cutar ta yi ajalin sama da yara 200 cikin mako biyu inda ya ce haƙiƙanin adadin shi ne 85.

Ya kuma ce fiye da marasa lafiya 2,510 da suka kamu da cutar a jihar sun samu sauƙi kuma an sallame su daga asibiti.

KU KUMA KARANTA: Gwamnati ta musanta mutuwar mutum 200 sanadiyar baƙuwar cuta a Yobe

Dakta Gana ya kuma ce an tura jami’an lafiya na sa kai sama da 200 zuwa sassan ƙananan hukumomin Potiskum da Fika a wani ɓangare na ƙoƙarin da ma’aikatar take na daƙile cutar.

Ya ce ma’aikatan lafiya sun bi gida-gida domin ganowa tare da tura mutanen da ke da cutar asibiti.

Yankunan arewacin Najeriya na fama da matsanancin zafi a tsukin nan, yanayin da ke haddasa cutar ta sanƙarau.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like