Connect with us

Kasashen Waje

Kotun duniya ta umurci Isra’ila ta dakatar da kai farmaki a Rafah

Published

on

Kotun duniya ta umurci Isra’ila ta dakatar da kai farmaki a Rafah

A ranar Juma’a ne babban kotun duniya ICJ ta umarci Isra’ila da ta dakatar da hare-haren da take yi a Rafah, birnin da ke kudancin Gaza inda Falasɗinawa sama da miliyan ɗaya suka nemi mafaka a cikin mawuyacin hali.

Ko da yake da wuya Isra’ila ta bi wannan umarni, wanda babbar kotun Majalisar Ɗinkin Duniya ba ta da hurumin aiwatar da shi, amma hukuncin da aka yanke zai ƙara matsin lamba kan ƙasar.

A ci gaba da ƙalubalantar ɓacin ran da ƙasashen duniya suka yi kan rikicin jin kai a yankin, sojojin Isra’ila sun ci gaba da kai munanan hare-haren da suka ƙaddamar sakamakon hare-haren Hamas na ranar 7 ga watan Oktoba.

KU KUMA KARANTA:Babbar Kotun MƊD ta fara sauraron ƙara kan afka wa Rafah da Isra’ila ta yi

Tattaunawar tsagaita buɗe wuta ta ci tura, duk da matsin lamba da ake yi a gida na firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu na ganin an sako mutanen da a ka yi garkuwa da su a Gaza.

Umurnin na ICJ ya biyo bayan roƙon gaggawa da ƙasar Afirka ta Kudu ta gabatar a wani ɓangare na shari’ar da take ci gaba da yi a kotun da ke birnin Hague na ƙasar Netherlands, inda ta zargi Isra’ila da aikata kisan kiyashi a hare-haren da ta shafe watanni ana kai wa Gaza, zargin da Isra’ila da Amurka suka musanta.

Mai yiyuwa ne shari’ar za ta ɗauki shekaru ana warwarewa, amma Afirka ta Kudu ta nemi umarnin wucin gadi don kare Falasɗinawa.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Sojojin Isra'ila sun ce an yi musayar wuta da dakarun Masar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kasashen Waje

Sojin Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo sun daƙile yunƙurin juyin mulki

Published

on

Sojin Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo sun daƙile yunƙurin juyin mulki

Jamhuriyar Dimokaraɗiyar Congo ta ce ta daƙile wani yuƙurin   kifar da gwamnatin shugaba Felix Tshisekedi a Kinshasha, kuma har da ƴan  ƙasashen waje a cikin masu wannan yunƙuri.

Lamarin ya auku ne da safiyar Lahadi a kusa da gidan ministan tattalin arzikin ƙasar, Vital Kamerhe, a yankin Gombe da ke arewacin babban birnin ƙasar, kamar yadda rahotanni  suka bayyana.

A jawabin da ya gabatar ga al’ummar ƙasar, kakakin rundunar sojin ƙasar, Janar Sylvain Ekenge ya tabbatar da lamarin, inda ya ce an kashe jagoran masu yukurin juyin mulkin, tare da kama mutane 50 da ke da hannu a ciki da suka haɗa  da wasu Amurkawa da dama da wani ɗan Birtaniya guda.

KU KUMA KARANTA:Da gaske ne an yi yunƙurin juyin mulki a Congo Brazzaville?

Janar Ekenge ya ce ɗan ƙasar Congon da ya jagoranci yunƙurin kifar da gwamnatin shine, Christian Malanga, wanda ya ke da takardar zaman ɗan Amurka, kuma tuni dakarun Congo su ka kashe shi.

Majiyoyi da dama sun bayyana cewa an ji ƙararraƙinharbe-harbe a kusa da fadar shugaban ƙasar a lokacin yunƙurin juyin mulkin.

Jakadan Amurka a Kinshasha ya bayyana kaɗuwarsa a kan lamarin da ya auku, a yayin da Tarayyar Afrika ta caccaki yunƙurin na kifar da gwamnatin farar hula.

Masu yunƙurin juyin mulkin sun shirya kai farmaki gidan sabuwar fira ministar ƙasar, Judith Suminwa, da kuma na mministan tsaro, Jean-Pierre Bemba, amma kuma sai suka gaza gane gidan Suminwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Real Madrid ta lashe kofin Laliga a karo 36

Published

on

Nasarar na zuwa ne bayan da ‘yan wasan Carlo Ancelotti suka lallasa Cadiz da ci 3-0 a ranar Asabar yayin da Barcelona ta sha kaye a hannun Girona da ci 4-2.
Real Madrid ta lashe kofin gasar La Liga a ƙasar Sifaniya a karo na 36 bayan da ta ba Girona ratar maki 13 a gasar.

Madrid tana da kwantan wasanni huɗu a yanzu haka duk da ta lashe kofin.

KU KUMA KARANTA:Babu rashin jituwa tsakanina da Salah – Klopp

Nasarar na zuwa ne bayan da ‘yan wasan Carlo Ancelotti suka lallasa Cadiz da ci 3-0 a ranar Asabar yayin da Barcelona ta sha kaye a hannun Girona da ci 4-2.

Da a ce Barcelona ta lashe wasanta da Girona, da Madrid ba ta samu nasarar ba a ranar Asabar.

Girona dai ta dage sai da ta ture Barcelona zuwa matsayi na uku a teburin gasar wacce ke da tazarar maki 14 tsakaninta da Madrid.

A ranar Laraba Madrid za ta karɓi bakuncin Bayern Munich a gasar cin kofin zakarun nahiyar turai a wasan semi-final.

A karawar farko da Madrid ta bi Bayern gida, an tashi da ci 2-2.

Continue Reading

Al'ajabi

Ɗan Ghana ya kafa tarihi na rungumar bishiyoyi a duniya

Published

on

Wani ɗalibi ɗan gwagwarmayar kare muhalli da gandun daji a Ghana ya kafa tarihin rungumar bishiyoyi masu yawa cikin sa’a ɗaya.

Kundin Adana Kayan Tarihi na Guinness ya wallafa a shafinsa cewa Abubakar Tahiru, mai shekara 29 ya rungumi bishiyoyi 1,123 cikin sa’a guda.

Abubakar ya taso ne a garin Tepa da ke albarkatun noma a Ghana, inda ya samu sha’awar abubuwan da suka shafi gandun daji da yanayi.

KU KUMA KARANTA:Ƙasashen Ghana da Kenya sun rattaɓa hannu kan yarjejeniyar haɗin gwiwa

Bayan kammala karatunsa na digirin farko a fannin gandun daji a ɗaya daga cikin manyan jami’o’in Ghana, Abubakar ya ci gaba da karatu a fannin gandun daji a jami’ar Auburn da ke jihar Alabama da ke Amurka a shekarar da ta gabata.

Ya kafa tarihin ne a gandun dajin Tuskegee, ɗaya daga cikin manyan gandun daji mai albarkatun bishiyoyin timber da ake katako da ita, a jihar ta Alabama.

Yadda yake rungumar bishiyoyin shi ne yakan rungume duka hannayensa a jikin bishiyar, kuma babu bishiyar da ya runguma fiye da sau ɗaya, kuma babu wata illa za dai yi wa bishiyar sakamakon rungumar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like