No menu items!

Sample Page Title

Date:

Kotun ƙolin masana’antu ta ƙasa da ke Abuja ta umarci GTBank da ta biya korarren shugaban hukumar ƙorafe-ƙorafen jama’a da yaƙi da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, Muhuyi Magaji Rimingado, kuɗi Naira Miliyan 5,713,891.22 daga asusun albashi na gwamnatin jihar.

Adadin kuɗaɗen da Rimingadon yake bi ne na albashin ma’aikata, bayan dakatar da shi a watan Yulin 2021.

Jaridar DAILY NIGERIAN ta ruwaito cewa gwamnatin jihar ta dakatar da Muhuyi Rimingado bayan buɗe bincike kan wasu kwangiloli da ake zargin an baiwa wasu kamfanoni masu alaƙa da iyalan gwamnan.

KU KUMA KARANTA: An maka magini a kotu, bisa laifin satar buhunan siminti 50

A zaman da aka ci gaba da yi a ranar Talatar da ta gabata, bankin ta bakin lauyansa Joshua Shekwolo ya shaida wa kotun a cikin wata takardar rantsuwa cewa gwamnatin jihar Kano ta na da asusun ajiyar banki da jimillar kuɗaɗen da suka kai N5,713,891.22 kasancewar an toshe hukuncin da aka yanke kan lamarin a cikin asusun.

Da yake bayar da cikakkiyar umarnin, mai shari’a O.O Oyewumi ya umarci GTBank ta biya kuɗin a asusun Rimingado cikin sa’o’i 48.

An bayar da umarnin ne bayan gazawar gwamnatin jihar wajen mutunta hukuncin da kotun ta yanke a ranar 14 ga Disamba, 2022, inda ta bayar da umarnin biyan da kuma amincewa da Rimingado a matsayin ƙwararren shugaban hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...