Kotu ta ci tarar ‘yan sanda naira miliyan 100 bisa kashe almajirin Shaikh Zakzaky ba bisa ƙa’ida ba

Mai shari’a Z. B. Abubakar na babbar kotun tarayya da ke Abuja, a ranar Litinin, 22 ga watan Mayu, 2023, ya bayyana cewa jami’an ‘yan sandan Najeriya sun kama wani ɗan ƙungiyar Harkar Musulunci a Najeriya, Ja’afar Muhammad a asibitin koyarwa na Gwagwalada a watan Yuli. 22 ga Yuli, 2019 da kashe shi a ranar 24 ga Yuli, 2019 a SARS Abattoir, Abuja.

Kotun ta bayyana hakan a matsayin taka doka, kuma ya zama babban take haƙƙinsa na asali kamar yadda sashe na 33 (1) 35 na Kundin Tsarin Mulki na 1999 ya tanada Tarayyar Najeriya (kamar yadda aka gyara).

Alƙalin kotun, yayin da yake yanke hukunci kan ƙarar da Naziru Isah Abdullahi ya shigar mai lamba FHC/ABJ/CD/409/2020, ya bayyana cewa, “Naziru Isah ya tabbatar da cewa ‘yan sanda sun harbe ɗan uwansa Ja’afar Muhammad, kuma sakamakon haka, ya samu rauni a lokacin da yake gudanar da Muzaharar lumana ta asaki Zakzaky a Sakatariyar Tarayya, Abuja, a ranar 22 ga Yuli, 2019.

KU KUMA KARANTA: Muna da ‘yancin mallakar muhalli don gudanar da rayuwarmu – Martanin almajiran Shaikh Zakzaky ga El-Rufai

“An kai Ja’afar asibitin koyarwa na Gwagwalada domin jinya. Yayin da yake asibitin da aka ce, ‘yan sanda sun mamaye asibitin, suka ɗauke shi, suka kai shi sashin SARS Cell, Abattoir, Garki, Abuja.

Yayin da yake hannun ‘yan sanda, Ja’afar Muhammad ba a bashi wani magani ba, wanda hakan ya sa ya mutu a ranar 24 ga Yuli, 2019.

Alƙalin ya kuma bayyana cewa, bayan rasuwar Ja’afar Muhammad, an ajiye gawarsa a Asibitin Asokoro dake Abuja.

“Kotu ta bayar da umarnin babban sufeton ‘yan sanda da kuma Daraktan kula da lafiya na asibitin gundumar Asokoto da su saki gawar Ja’afar Muhammad ga iyalansa domin yi musu jana’iza cikin gaggawa kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Kotun ta kuma bayar da umarnin cewa Sufeto Janar na ‘yan sandan ƙasar ya biya tarar kuɗi 100,000,000.00 (Naira Miliyan Ɗari) kawai saboda tsarewa da kashe Ja’afar Muhammad ba bisa ƙa’ida ba.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *