No menu items!

Sample Page Title

Date:

Kotu a Kano ta tura matasan da suka yi yunƙurin hana zance a Unguwar Ja’en Gidan Yari

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Kotun shariʼar musulunci da ke Kofar Kudu a Kano karkashin mai shariʼa Shamsuddeen Ado Abdullahi Unguwar Gini ta aike da wasu matasa 2 gidan yari saboda sassara wani saurayi da ya je zance unguwar Jaʼen da adda.

Kungiyar ci gaban alʼummar Jaʼen ce ta yi karar matasan Usman Rabiʼu Usman da Aliyu Rabiʼu Usman kan zarginsu da saka dokar ta baci ta hana yin zancen saurayi da budurwa.

KU KUMA KARANTA: Hisbah a Kano za ta fara kamen masu hira da mata a cikin mota

Mai gabatar da kara, lauyar gwamnatin Kano Baristar Aliya Aminu Yargata ta karanta musu zargin amma sun musanta, sai dai ta nemi a basu wata ranar don kawo shaidu.

Lauyan wadanda ake kara Barista Jamilu Jaʼafar ya roki a ba da belinsu, amma kotun ba ta amince ba.

Kotun ta turasu gidan yari gar zuwa 22 ga watan Mayun da muke ciki, don ci gaba da shariʼa.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...