No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jam’iyar APC ta dakatar da tsohon Gwamnan jihar Ogun, Gbenga Daniel bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

Jam’iyyar APC reshen Jihar Ogun ta dakatar da tsohon gwamnan jihar kuma Sanatan Ogun ta tsakiya , Gbenga Daniel, har abada bisa zargin yin ayyukan da suka saba wa jam’iyya.

Dakatarwar, wadda ta haɗa da Kunle Folarin – ɗaya daga cikin magoya bayansa – ta samu amincewar kwamitin gudanarwa na jihar bayan mazabu nasu a Shagamu sun zarge su da aikata “ayyukan adawa da jam’iyya.”

APC ta bayyana cewa an gayyaci Daniel da Folarin domin kare kansu, amma sun ki bayyana a gaban kwamitocin ladabtarwa.

KU KUMA KARANTA: Ganduje ya Ajiye mukaminsa na Shugabancin Jam’iyar APC na Ƙasa

Haka kuma jam’iyyar ta zarge su da tsoratar da ‘yan jam’iyya tare da matsa musu lamba su janye ƙorafe-ƙorafen da aka shigar a kansu.

Ana hasashen wannan mataki na iya daɗa rura rikicin siyasa tsakanin Daniel da gwamnan Ogun na yanzu, Dapo Abiodun, musamman bayan gwamnatin jihar ta sanya alamar rushewa a wasu kadarori da ake danganta da Sanatan.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...