No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jami’ar Columbia ta yi barazanar korar ɗaliban da ke zanga-zangar adawa da hare-haren da Isra’ila take kai wa Gaza.

Jami’ar ta ce ɗaliban da ke zaman dirshan a wani ginin harabar makarantar a matsayin zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu, na fuskantar korar daga karatunsu, saboda sun karya doka.

KU KUMA KARANTA: Ɗalibai a faɗin Amurka na ci gaba da yin zanga-zangar nuna adawa da yaƙin Isra’ila a Gaza

“Ɗaliban da suka mamaye ginin na fuskantar kora,” in ji ofishin kula da harkokin jama’a na Columbia a cikin wata sanarwa, inda ya ƙara da cewa an ba masu zanga-zangar “damar fita cikin lumana” amma a maimakon haka suka ƙi tare da kara ta’azzara lamarin.

Ana kallon wannan a matsayin keta hakkin ɗaliban da ƙoƙarin hana su faɗin albarkacin bakinsu a ƙasar da take iƙirarin kare ƴancin ɗan’adam.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...