Iyayen yara sun nemi ɗaukin Gwamnatin Kano akan Makarantar Sakandiren Kwakwaci da ta lalace

0
0

Iyayen yara sun nemi ɗaukin Gwamnatin Kano akan Makarantar Sakandiren Kwakwaci da ta lalace

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Makarantar sakandire ta kwakwaci, guda ce daga cikin manyan makarantu a yankin karamar hukumar Fagge.

Bayan koken iyayen yaran wannan yankin, wakilin Jaridar Neptune Prime a Kano, ya je wannan makaranta, sai dai wannan makaranta na cikin mawuyacin hali yanzu haka.

Makarantar ta zama mafakar ɓata gari, wanda suke shiga suke aikata shaye-shaye, da harkar sayar da kayan maye.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Kano ta rufe wasu rumfuna

Wasu kuma suna shiga suna kashi a ciki, al’ummar wannan yanki da iyayen dalibai sunyi kira ga Gwamnatin Kano da ta kai agajin gaggawa wannan makaranta,

Domin wajen na barazana ga tarbiyya yara, a gefe guda kuma suna bukatar gyara azuzun domin yara su sami isasshen muhalin karatu.

Leave a Reply