Iyayen yara sun nemi ɗaukin Gwamnatin Kano akan Makarantar Sakandiren Kwakwaci da ta lalace

0
101
Iyayen yara sun nemi ɗaukin Gwamnatin Kano akan Makarantar Sakandiren Kwakwaci da ta lalace

Iyayen yara sun nemi ɗaukin Gwamnatin Kano akan Makarantar Sakandiren Kwakwaci da ta lalace

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Makarantar sakandire ta kwakwaci, guda ce daga cikin manyan makarantu a yankin karamar hukumar Fagge.

Bayan koken iyayen yaran wannan yankin, wakilin Jaridar Neptune Prime a Kano, ya je wannan makaranta, sai dai wannan makaranta na cikin mawuyacin hali yanzu haka.

Makarantar ta zama mafakar ɓata gari, wanda suke shiga suke aikata shaye-shaye, da harkar sayar da kayan maye.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Kano ta rufe wasu rumfuna

Wasu kuma suna shiga suna kashi a ciki, al’ummar wannan yanki da iyayen dalibai sunyi kira ga Gwamnatin Kano da ta kai agajin gaggawa wannan makaranta,

Domin wajen na barazana ga tarbiyya yara, a gefe guda kuma suna bukatar gyara azuzun domin yara su sami isasshen muhalin karatu.

Leave a Reply