No menu items!

Sample Page Title

Date:

Iyayen ɗaliban da aka sace a Jami’ar Tarayya da ke Gusau a jihar Zamfara sun gudanar da zanga-zangar lumana a gidan gwamnatin jihar, suna neman a sako ’ya’yansu ba tare da wani sharaɗi ba.

Sun buƙaci Gwamna Dauda Lawal da jami’an tsaro su ceto ’ya’yansu da aka yi garkuwa da su tsawon kwanaki 72 ba tare da wani abu ya same su ba.

Masu zanga-zangar sun sha alwashin ci gaba da zama a gidan gwamnatin Jihar Zamfara har sai an sako ’ya’yansu.

Sun ce ’yan bindigar sun tuntuɓi wasu daga cikinsu kuma sun bayar da sharaɗin tattaunawa da gwamnatin jihar kafin sakin ɗaliban.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun ƙara sace ɗaliban jami’ar Zamfara

A ranar 22 ga watan Satumba ne ’yan bindiga suka yi garkuwa da ɗaliban jami’ar kimanin 24 tare da wasu ma’aikata a jami’ar.

Sai dai an ƙubutar da ɗalibai 13 da ma’aikatan gini uku yayin da har yanzu raguwar suke tsare a hannun ’yan bindigar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...