No menu items!

Sample Page Title

Date:

INEC ta sanya ranar 16 ga Agusta don zaɓen cike gurbi a mazabu 16

Daga Shafaatu Dauda Kano

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta sanar da cewa za ta gudanar da zaɓukan cike gurbi a ranar Asabar, 16 ga Agusta, 2025, domin cike guraben kujeru a majalisun tarayya da na jihohi a faɗin jihohi 12 a Najeriya.

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ne ya bayyana haka yayin wata ganawa da shugabannin jam’iyyu a Abuja ranar Alhamis 25 ga Yuni, 2025.

Zaɓukan cike gurbin za su gudana ne domin cike guraben kujeru a Majalisar Tarayya da kuma Majalisun Dokoki na Jihohi, sakamakon murabus, rasuwa ko kuma soke zaɓe da kotu ta yi.

“Zaɓukan za su gudana a mazabu 16, ciki har da gundumomi biyu na Sanata, gundumomi biyar na majalisar wakilai, da kuma kujeru tara na majalisun jihohi,” in ji Yakubu.

KU KUMA KARANTA:Kotu tayi watsi da hukuncin zaɓen ƙananun hukumomin jihar Kano

Mazabun da za a gudanar da zaɓe sun haɗa da:

Sanatoci: Anambra ta Kudu da Edo ta Tsakiya

Majalisar Wakilai: Ovia South West/Ovia South East (Edo), Babura/Garki (Jigawa), Chikun/Kajuru (Kaduna), Ikenne/Shagamu/Remo North (Ogun), da Ibadan North (Oyo)

Majalisun Jihohi: Ganye (Adamawa), Onitsha North I (Anambra), Dekina/Okura (Kogi), Zaria Kewaye da Basawa (Kaduna), Bagwai/Shanono (Kano), Mariga (Niger), Karim Lamido I (Taraba), da Kauran Namoda South (Zamfara)

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...