No menu items!

Sample Page Title

Date:

A ranar talata ne Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Ta’annati (EFCC), ta gurfanar da tsohon gwamnan jihar Benue, Samuel Ortom, na tsawon sa’o’i tara kafin daga bisani a sake shi.

Ortom ya isa harabar hedikwatar hukumar, Makurɗi, da ƙarfe 10 na safe kuma ya bar wurin da misalin ƙarfe 7:00 na yamma.

Da yake mayar da martani, mai taimaka wa Mista Ortom kan harkokin yaɗa labarai, Terver Akase, ya ce saɓanin yadda ake zarge-zarge a wasu sassan kafafen yaɗa labarai, ba a kama tsohon gwamnan ba sai dai ya mutunta gayyatar da hukumar ta yi masa.

“Ba a kama Ortom ba kuma ba a tsare shi a hedikwatar EFCC da ke Makurɗi, ba” in ji Mista Akase.

KU KUMA KARANTA: EFCC ta kama ma’aikatan FMC 50 bisa zargin zamba ta intanet a jihohin Ogun da Oyo

A cewarsa, tsohon gwamnan ba shi da wani abin ɓoyewa, inda ya ƙara
da cewa zai kasance a ko da yaushe domin amsa tambayoyi daga hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

“Ortom ba shi da wani abin da zai ɓoye game da shugabancinsa a jihar,” in ji Mista Akase.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...