No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar haɗin gwiwar Hisbah da ’yan sanda da hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi (NDLEA) ta cafke wasu mutane 37 bisa zargin su da yin karuwanci da sayar da giya a Damaturu babban birnin Jihar Yobe.

Muƙaddashin kwamandan Hisbah na jihar, Mohammed Murtala Goni Ahmed, ya ce an kama mutanen ne a Zango, Maina Lodge, Ajayi, Bakin Kasuwa da kuma Bakin Tasha a Damaturu.

Da yake gabatar da waɗanda ake zargin a ofishin rundunar ’yan sandan jiar, ya bayyana cewa mata 17 da maza 20 masu shekaru tsakanin 15 zuwa 18 suka shiga hannu a samamen.

KU KUMA KARANTA: Hisbah ta kori jami’inta kan haɗa kai da masu baɗala a Kano

“Binciken da aka gudanar a kan waɗanda ake zargin ya kuma nuna cewa, a cikin mazan, an same su da yawa suna sayar da ƙwayoyi sannan kuma an same su da kiret 50 na kwalaben giya,” in ji Goni.

Wasu daga cikin waɗanda ake zargin da suka zanta da Aminiya sun ce an kama su ne bisa kuskure domin ba su da laifin abin da ake zargin su da shi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...