Connect with us

Hatsari

Hatsarin kwale-kwale ya yi sanadin mutuwar sama da mutum 90 a Mozambik

Published

on

Mutum fiye da 90 ne suka mutu yayin da wani kwale-kwale maƙare da jama’a ya kife a arewacin Mozambik, a cewar hukumomi ranar Lahadi.

Kwale-kwalen, wanda na kamun kifi ne ɗauke da mutum aƙalla 130, ya kife ne a lokacin da yake ƙoƙarin isa wani tsibiri da ke lardin Nampula, in ji wasu jami’an gwamnati.

Sakataren jihar Nampula, Jaime Neto ya ce, “Ya nitse ne sakamakon lodin da aka yi masa wanda ya wuce ƙima. Fasinjoji 91 ne suka mutu.”

Ya ƙara da cewa ƙananan yara da dama na cikin waɗanda suka mutu.

Masu aikin ceto sun kuɓutar da mutum biyar da ransu kuma suna ci gaba da neman ƙarin mutanen da lamarin ya shafa, amma suna fuskantar ƙalubale sakamakon rashin yanayi mai kyawu.

Neto ya ce akasarin mutanen da ke cikin kwale-kwalen suna ƙoƙarin tserewa daga yankin ne sakamakon wani labarin ƙarya da aka riƙa yaɗawa cewa cutar kwalara ta ɓarke a yankinsu.

KU KUMA KARANTA: Mutane 20 sun mutu a wani kwale-kwale da ya nutse a gaɓar tekun Senigal

Bayanan da gwamnatin Mozambik ta fitar sun nuna cewa mutum kimanin 15,000 ne suka kamu da cutar kwalara inda 32 daga cikinsu suka mutu tun daga watan Oktoba.

A watannin baya-bayan nan, mutane sun riƙa tserewa zuwa yankin na Nampula sakamakon hare-haren ƴan bindiga da suke fuskanta a yankin Cabo Delgado da ke maƙwabtaka.

Neto ya ce an soma gudanar da bincike don gano musabbabin kifewar kwale-kwalen.

Ya ƙara da cewa biyu daga cikin mutanen da aka ceto suna samun kulawa a asibiti.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hatsari

Jirgin sojin Najeriya ya faɗo a Kaduna

Published

on

Jirgin sojin Najeriya ya faɗo a Kaduna

Jirgin sojin Najeriya ya faɗo a Kaduna

Wani jirgin sama na sojin Najeriya ya yi hatsari a ƙauyen Tami da ke yankin Karamar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna.

Wani mazaunin yankin ya ce jirgin sojin mai sauƙar ungulu ne, kuma ya yi hatsari ne da misalin karfe 5 na asubar Litinin din nan.

Mazauna yankin sun bayyana cewa matukin ya fito daga cikin tarkacen jirgin da ya fado.

Bayan nan sojoji suka yi gaggawar zuwa suka yi wa yankin kawanya tare da fara bincike.

Sojojin sun kuma hana mutane isa wurin da tarkacen jirgin yake.

KU KUMA KARANTA: Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin jirgin samanta

An ce jirgin yana tsaka da aikin sintiri a yankin ne ya samu matsala, lamarin da ya haddasa faduwarsa.

Kawo yanzu Hedikwatar Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ba ta fitar da sanarwar game da lamarin ba.

Continue Reading

Hatsari

Wani mummunan hatsari yayi sanadiyyar mutuwar mutane 16 daga cikin 18 da ke motar

Published

on

Wata motar fasinja da ta taso daga Bauchi ta yi hatsari a Inugu kuma mutum 16 daga cikin fasinjoji 18 dake motar maza 14 mata 2 sun mųțtu, wasun su ma ba a iya gane su don sun ƙone ƙurmus.

‘Yan sanda sun ce lamarin ya faru da yammacin jiya Talata, 30 ga watan Afrilu a babban titin garin Ekwegbe.

KU KUMA KARANTA: Fasinjoji sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Kogi

Motar ƙirar Toyota Hummer Bus ce 18 seater dauke da lambar Bauchi, DAS 215 XA, kuma an rubuta “Masha Allah” a jikin motar.

Don haka Kwamishinan yan sanda na Enugu ke roƙon jama’a duk wanda Allah yasa ya san wani daga cikin fasinjojin to a tuntubi rundunar a 08098880172 ko 08086671202

Continue Reading

Gobara

Mutane da dama sun mutu, sakamakon fashewar tankar mai a Fatakwal

Published

on

Ana fargabar mutane da dama sun rasa rayukansu bayan da wata tankar mai ta kama da wuta a hanyar East-West Road a birnin Fatakwal da ke jihar Rivers a kudancin Najeriya.

Jaridun Punch da na Vanguard sun ruwaito cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:45 na daren Juma’a.

Bayanai sun yi nuni da cewa bayan da tankar ta mai ta kama da wuta, ta shafi motoci aƙalla goma da ke jerin cunkoson ababen hawa a birnin na Fatakwal.

KU KUMA KARANTA:Matatar man Fatakwal za ta koma bakin aiki cikin watan Afrilu – Kyari

Wani da ya shaida lamarin ya faɗawa jaridar Vanguard cewa ya ji ƙara har sau biyu masu firgitarwa daga baya kuma hayaƙi ya turnuƙe sararin samaniya.

“Idan kuna da ‘yan’uwa a Fatakwal ku ƙira su don ku ji lafiyarsu” Wani mazaunin birnin na Fatakwal mai suna Bassey Esang Don, ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto ba a san musabbabin fashewar da ta auku ba ko iya sanin adadin mutanen da suka mutu.

Faɗuwar tankar mai ta kama da wuta ba baƙon abu ba ne a Najeriya, inda a wasu lokuta mutane kan yi rububin zuwa kwasar man idan yana Malala.

Daga nan ne kuma akan samu akasi har wuta ta kama ta laƙume rayukan mutane.

Wannan al’amari na faruwa ne yayin da farashin mai ya ƙara tsada a Najeriya inda litar mai ta kusa kai wa Naira 1,000 a sassan ƙasar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like