No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnonin Jihohin Arewa 19 da Sarakunan Gargajiya suyi taro a Kaduna

Daga Idris Umar,Zariya

Gwamnonin jihohin Arewa guda 19 sun gudanar da muhimmin taro tare da manyan sarakunan gargajiya daga yankin Arewa, a wani yunkuri na fuskantar matsalolin tsaro, tattalin arziki, da ci gaban al’umma. Taron ya gudana a birnin Kaduna, karkashin jagorancin Gwamnan jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, wanda ke shugabantar kungiyar Gwamnonin Arewa.

KU KUMA KARANTA:Taron Gwamnonin Arewa Maso Gabas: Dole ne mu ƙarfafa haɗin kai don dakatar da matsalar tsaro – Gwamna Buni

Haka zalika, Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, wanda shi ne shugaban majalisar koli ta addinin Musulunci a Najeriya, ya kasance a sahun gaba wajen jagorantar bangaren sarakunan gargajiya a taron.

Taron ya kunshi tattaunawa kan hanyoyin da za a bi don tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a yankin Arewa, da kuma hanyoyin karfafa hadin kai tsakanin gwamnoni da sarakunan gargajiya domin cimma burin ci gaban yankin gaba ɗaya.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...