No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana dalilin rufe wasu kasuwannin dabbobi a jihar.

Alfijir labarai ta rawaito a ranar Laraba ne gwamnatin jihar ta sanar da rufe kasuwannin a ƙananan hukumomi bakwai waɗanda ta ce ana hada-hadar shanu da dabbobin sata.

Mannir Haidara Kaura, kwamishinan watsa labarai da raya al’adu na jihar, ya bayyana wa BBC Hausa cewa an ɗauki wannan mataki ne a wani yunƙuri na tabbatar da kare rayuka da dukiyoyin jama’ar jihar.

Ya ce bayanan da gwamnati da hukumomin tsaro suka samu sun nuna cewa ‘yan fashin daji na shigo da dabbobin da suka ƙwace a hannun mutane suna cinikinsu inda suke samun kuɗin da suke gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

KU KUMA KARANTA: ’Yan bindiga a Taraba sun sace mutane ana tsaka da cin kasuwa

Yanayi na tsaro abu ne da ke da sarƙaƙiya, amma dai muna ganin matakan da wannan gwamnati ke ɗauka za su fara tasiri ba da jimawa ba, domin za mu toshe musu wannan kofa” in ji kakakin gwamnatin

Ba dai wannan ne karon farko da gwamnatin jihar ta Zamfara ke rufe kasuwannin dabbobi ba, bisa zargin hada-hadar dabbobin sata da ‘yan fashin daji ke kawowa.

A watan Satumba ma akwai wasu kasuwanni guda bakwai da gwamnatin jihar ta rufe saboda irin wannan zargi, inda ake ci gaba da bincike.

Jihar Zamfara dai na ɗaya daga cikin jihohin da suka fi fama da matsalar tsaro a Najeriya, inda yan fashin daji ke kai hare-hare, suna kashe jama’a da kuma satar dukiyoyinsu, ciki har da dabbobi.

Sai dai gwamnatin jihar na ganin cewa irin waɗannan matakai da take ɗauka, za su taimaka wajen shawo kan matsalar da ta ki ci ta ki cinyewa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...