No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa za ta mayar da shalkwatar hukumar kula da filayen jiragen saman ƙasar (FAAN) zuwa birnin Lagos

Matakin na ƙunshe cikin wata sanarwa da babbar daraktar hukumar Misis Olubunmi Kuku ta fitar.

Sanarwar ta ce ministan kula da sufurin jiragen sama na ƙasar ne ya bayar da umarnin ɗauke shalkwatar hukumar ta FAAN daga Abuja babban birnin ƙasar zuwa birnin Legas da ke kudu maso Yammacin ƙasar.

KU KUMA KARANTA: Hukumar FAAN ta hana tafiya da jakar ‘Ghana Must Go’ a filayen jirgin sama

Matakin na zuwa ne yayin da a farkon makonnan Babban Bankin ƙasar CBN ya sanar da ɗaukar matakin mayar da wasu sassan bankin zuwa birnin na Legas.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...