No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani magidanci mai suna Shu’aibu Ahmad mazaunin unguwar Tudun Wada Brigate a ƙaramar hukumar Nassarawa a birnin Kano, ya rasa ransa tare da matarsa Binta da ‘ya’yansu guda 5.

Hakan ya faru ne sakamakon tashin wata mummunar gobara da ta afku dalilin kawo wutar lantarki mai ƙarfin gaske da misalin ƙarfe 12 na daren Lahadin da ta Gabata.

Muneer Ibn Ibrahim shi ne mai gidan hayar da suke, ya sheda cewa, wani firinji ne yai sanadin tashin gobarar bayan ya kama da wuta a lokacin da aka kawo wutar, shi kuma marigayin da iyalansa suna bacci ɗakin nasu kuma a rufe.

KU KUMA KARANTA: Gobara ta cinye ɗaruruwan shaguna a kasuwar Gwarzo

Wannan dalilin ya jawo hayaƙi ya turniƙe su inda hakan yai sanadiyar mutuwarsu su bakwai lokaci ɗaya.

An yi jana’izarsu kamar ya addini ya tanadar.

Allah ya jikansu da rahama Allah ya kyautata makwancinsu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...