No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gobara ta ƙone gidan ƙaramar Ministar babban birnin tarayya, Abuja Dokta Mariya Mahmoud.

Gobarar ta tashi ne a ranar Lahadi, inda ta ƙone gidan ministar.

Gobarar ta tashi ne gidan ministar da ke yankin Asokoro da tsakar rana.

Rahotanni sun bayyana cewar jami’an kashe gobara ba su kai ɗauki a kan lokaci ba, lamarin da ya sanya gobarar yin ɓarna mai tarin yawa.

KU KUMA KARANTA: Gobara ta ƙone ofishin ‘yan sanda a Kano

Duk da babu cikakken rahoto game da gobarar, amma hadimin ministar kan kafafen watsa labarai, Mista Austine Elemue, ya tabbatar da faruwar lamarin, amma bai yi karin bayani ba.

Amma hadimin ya ce ana gudanar da bincike game da musababbin tashin gobarar a gidan ministar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...