Connect with us

Labarai

Gamayyar ƙungiyoyin farar hula ta Najeriya ta ɗorawa hukumomi alhakin rashin tsaro

Published

on

Daga Maryam Umar Abdullahi

Gamayyar ƙungiyoyin fararen hula sama da 40 sun kai ƙarar shugaban Najeriya Bola Tinubu, inda suka yi ƙira gare shi da ya magance matsalar rashin tsaro da ta ƙara ƙamari tun bayan hawansa mulki a watan Mayun da ya gabata.

Koken ya biyo bayan wasu sace-sacen da aka yi a babban birnin tarayya Abuja da kuma jihar Ekiti da ke kudu maso yammacin ƙasar.

A wani rahoto da gamayyar ƙungiyoyin farar hula suka fitar a wannan makon, an bayyana cewa, an kashe aƙalla mutane 2,400 tare da yin garkuwa da wasu kusan 1,900 tun watan Mayun bara lokacin da Tinubu ya karɓi mulki.

Ƙungiyar ta ce ta damu matuƙa da taɓarɓarewar tsaro a faɗin Najeriya inda ta yi ƙira ga hukumomi da su ɗauki matakan da suka dace don magance matsalar.

Auwal Rafsanjani, babban daraktan cibiyar kare haƙƙin fararen hula, wanda ya yi magana a madadin ƙungiyar ya ce, “Rashin tsaro ya mamaye ƙasarmu, ‘yan ta’adda sun mamaye ƙasarmu, ‘yan fashi da makami, ‘yan bangar siyasa, ana kashe ‘yan Najeriya kamar tururuwa, kowace ranar da kuka farka, sai dai a ji kisa bayan kisa, ba za mu iya ci gaba da zama a haka ba.”

Rahoton ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da kai munanan hare-hare a ƙasar ciki har da Abuja.

A birnin Abuja, wasu gungun masu ɗauke da makamai sun kai hare-hare na garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa a makonnin da suka gabata. An kashe mutane biyu daga iyalai daban-daban a matsayin gargaɗi ga waɗanda ba su biya ba.

KU KUMA KARANTA: Ƙungiyar kare ‘yancin Musulmi ta MURIC, ta soki kwamitin da gwamnatin Filato ta naɗa don warware rikicin Mangu

A jihar Ekiti da ke kudu maso yammacin ƙasar, a kwanakin baya wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban makaranta shida da malamai uku. Hari ila yau, a ranar, wasu ‘yan bindiga suka kuma kai hari a wasu ƙauyukan jihar tare da kashe wasu sarakunan gargajiya guda biyu.

Tinubu ya yi Allah-wadai da hare-haren sannan ya umarci jami’an tsaro da su kamo waɗanda suka kai harin.

Sai dai wani mai sharhi kan harkokin tsaro Chidi Omeje ya ce gazawar gwamnati ce ta haifar da matsalar da ake fama da ita.

Tushen duk waɗannan abubuwa shi ne rashin shugabanci, rashin shugabanci ke haifar da talauci, takaici, da fushin jama’a, in ji shi. “Duba, akwai alaƙa tsakanin talauci, rashin shugabanci da kuma yaɗuwar aikata laifuka.”

A bara, Tinubu ya sha alwashin magance matsalolin tsaro a Najeriya idan har aka zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa.

Bayan hawansa mulki, Tinubu ya yi wa wasu hafsoshi ritaya tare da naɗa sabbi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like