Rasuwa
Fitaccen ɗan wasan barkwanci na Najeriya, John Okafor, ya mutu
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/Screenshot_20240303-075830_1.jpg)
Fitaccen ɗan wasan barkwanci na Najeriya, John Okafor, wanda aka fi sani da Mr Ibu, ya mutu yana da shekaru 62, kamar yadda Ƙungiyar Ƴan Wasan Kwaikwayo ta Najeriya ta tabbatar.
Mr Ibu ya rasu ne ranar Asabar a Asibitin Evercare da ke unguwar Lekki a birnin Lagos.
An garzaya da ɗan wasan kwaikwayon sashen bayar da kulawar gaggawa da rana, sai dai rai ya yi halinsa, in ji sanarwar da iyalansa suka fitar.
Shugaban Ƙungiyar Ƴan Wasan Kwaikwayo ta Nijeriya Emeka Rollas Ejezie, ya ce Mr Ibu ya mutu bayan ya yi fama da “bugun zuciya.”
KU KUMA KARANTA: Mutane 20 sun mutu a wani kwale-kwale da ya nutse a gaɓar tekun Senigal
Rollas, wanda ya tabbatar da rasuwar Mr Ibu a shafinsa na Instagram, ya ƙara da cewa Don Single Nwuzor, manajan da ya kwashe shekaru 24 yana aiki tare da Mr Ibu ne ya gaya masa rasuwar ɗan wasan kwaikwayon.
A watan Nuwamban 2023 ne aka yanke ɗaya daga cikin ƙafafun Mr Ibu sakamakon larurar da yake fama da ita a wancan lokacin.
A watan Disamba kuma, iyalan ɗan wasan kwaikwayon suka fitar da sanarwar da ke musanta cewa an yanke masa ƙafa ne sakamakon ciwon suga.
Ƙasashen Waje
Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu
![Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/IMG-20240702-WA0041.jpg)
Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu
Daga Ibraheem El-Tafseer
Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.
A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.
A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.
KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki
Rasuwa
Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa
![Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/IMG_6198-637x430-1.jpeg)
Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa
Hajiya Zainab ta rasu ne a asibiti bayan gajeruwar rashin lafiya.
Mutuwa ta riske ta ne a wani asibiti da ke Minna, babban birnin jihar a ranar Talata.
Gwamnan jihar, Mohammed Umaru Bago, ya bayyana alhini da game da wannan rashi.
Sakon ta’aziyyar da kakakinsa, Bologi Ibrahim, ya sa wa hannu ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga jihar.
KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa
Ya kuma yi addu’a Allah Ya sada ta da mafificin rahama a Aljanna Firdausi, Ya ba wa mijinta hakurin jure wannan rashi.
Rasuwa
Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa
![Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/Ali-Modu-Sheriffs-Mother-Dies-At-93-920x555-1.jpg)
Allah Ya yi wa mahaifiyar tsohon Gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff rasuwa
Mahaifiyar tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff ta riga mu Gidan Gaskiya.
Mahaifiyar tsohon gwamnan, Hajja Aisa, ta koma ta Mahaliccinta ne a ranar Lahadi a Maiduguri, babban birnin jihar.
Ta rasu tana da shekaru 93, bayan fana da rashin lafiya.
Sanarwar rasuwar ta bayyana cewa za yi jana’izar Hajja Aisa da Azahar ranar Litinin 1 ga watan Yuli, 2024.
KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa tsohuwar jarumar Kannywood, Fati Slow rasuwa
Za a yi jana’izar ne a gidant Marigayi Galadima Modu Sheriff d da ke Damboa Road a Maiduguri.
Sanarwar ta kuma roka wa marigayiyar gafara da kuma Aljannatul Firdaus.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano