Connect with us

EFCC

EFCC za ta gurfanar da sojojin saman Najeriya a kotu kan zargin damfara a intanet

Published

on

Hukumar da ke yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta’annati, EFCC, ta ce za ta gurfanar da wasu sojojin saman Najeriya a gaban kotu bisa zargin yin damfara a intanet.

Hukumar ta bayyana haka ne a wata sanarwa da ta fitar ranar asabar da maraice.

Sanarwar ta ce “Hukumar EFCC reshen jihar Kaduna za ta gurfanar da sojojin saman Najeriya da ta bayar da belinsu ranar Juma’a, 17 ga watan Nuwamba, 2023 a gaban kotu da zarar ta kammala binciken da take yi a kansu.”

“An saki sojojin ne zuwa ga hukumominsu bayan sun cika tsauraran dokokin bayar da beli na hukumar. Wannan hukuma tana jaddada cewa babu wanda ya fi karfin doka kuma za a bi kadin wannan lamari har karshensa,” in ji EFCC.

A ranar Juma’a ne aka samu hatsaniya tsakanin wasu sojojin Najeriya da jami’an EFCC bayan sun je ofishin hukumar na Kaduna domin ƙuɓutar da jami’ansu da aka kama bisa zargin yin damfara a shafukan intanet.

KU KUMA KARANTA: EFCC ta gurfanar da shugaban kamfanin man fetur a kotu kan damfarar biliyan huɗu

Lamarin ya tayar da ƙura sosai inda mutanen da ke yankin suka rika ranta a na kare. Tun da farko, EFCC ta sanar cewa ta kama “mutum biyar a gidan abinci na Inn and Disney Chicken Eatery a Barnawa da ke Kaduna bayan samun kwararan bayanan sirri a kan zargin suna aikata damfara da ta shafi intanet.”

Mutanen da ake zargi da damfarar sun haɗa da Favour Itung, Rachael Ande, Suleiman Haruna, Abubakar Ismaila da Solomon Olobatoke, kuma an kama su, in ji EFCC.

Hukumar ta ce bayan haka ne wasu sojoji da suka ga abin da ya faru da ‘yan uwansu, suka yi dirar mikiya a ofishin EFCC da ke Kaduna inda suka yi yunƙurin ƙuɓutar da waɗanda ake zargi da aikata damfarar intanet.

An kama su kuma an tsare saboda sun keta doka, a cewar EFCC.

Hukumar ta ƙara da cewa daga nan ta soma tattaunawa da rundunar sojin sama kan batun, amma abin takaici wasu sojoji sun sake zuwa ofishinta a cikin damarar yaƙi domin ƙuɓutar da ‘yan uwansu, lamarin da ya kawo hatsaniya.

Daga bisani an saki waɗanda aka kama, kuma EFCC ta ce za ta gurfanar da su a gaban ƙuliya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

EFCC

Kotu ta ƙwace dala milyan 4 da dubu 700 da naira miliyan 830 da sauran kadarori daga hannun Emefiele

Published

on

Kotu ta ƙwace dala milyan 4 da dubu 700 da naira miliyan 830 da sauran kadarori daga hannun Emefiele

Mai Shari’a Yellim Ɓagoro ne ya ba da umarnin a jiya Alhamis 23 ga watan Mayun da muke ciki, sakamakon buƙatar da lauyan Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yiwa tattalin arziƙin Najeriya zagon ƙasa, Bilkisu Buhari, ta gabatar.

Babbar Kotun Tarayya dake Legas ta ba da umarnin wucin gadi na ƙwace fiye da dala miliyan 4 da dubu 700 da naira miliyan 830, da sauran kadarori da dama dake da alaƙa da tsohon gwamnan Babban Bankin Najeriya, Mista Godwin Emefiele.

Mai Shari’a Yellim Ɓagoro ne ya ba da umarnin a jiya Alhamis 23 ga watan Mayun da muke ciki, sakamakon buƙatar da lauyan Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yiwa tattalin arziƙin Najeriya zagon ƙasa, Bilkisu Buhari, ta gabatar.

KU KUMA KARANTA:CBN ya ba bankuna umarnin saka sabon harajin tura kuɗi

Bayan sauraron lauyan Hukumar EFCC, a hukuncin da ta zartar, Mai Shari’a Yellim Ɓagoro ta ce, “na saurari hujjojin lauyan masu ƙara sa’annan na nazarci buƙatar da aka gabatar tare da takardun dake mara mata baya.

An bayyana cewar kuɗaɗen da za a mayarwa gwamnatin tarayya a matakin wucin gadin na ajiye ne a bankunan “First da Titan da Zenith waɗanda Omoile Anita Joy da kamfanonin “Deep Blue Energy Services Limited da Exactquote Bureau de Change Ltd da Lipam Investment Services Limited da Tatler Services Ltd da Rosajul Global Resources Ltd da kuma Til Communication Nigeria Ltd ke gudanar da su.

EFCC ta doshi kotu ne domin neman ƙwace kuɗaɗen a matakin wucin gadi, ƙarƙashin sashe na 17 na dokar yaƙi da zambar kuɗaɗe ta 14 ta 2006, da sashe 44(2)(b) na kundin tsarin mulkin Najeriya kuma ƙarƙashin hurumin kotun.

Continue Reading

EFCC

EFCC za ta gurfanar da Hadi Sirika kan zargin N2.7bn

Published

on

Yau Alhamis za a gurfanar da tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Sanata Hadi Sirika a gaban kotu, kan badaƙalar naira biliyan 2.7.

Hukumar Yaki da Masu Karya Arzikin Kasa (EFCC) za ta gurfanar da Hadi Sirika tare da ’yarsa Fatimah da wasu biyu ne kan badakalar kwangilar Naira biliyan 2.7 da aka bankado a ma’aikatar sufurin jiragen sama karƙashin jagorancin Sirika.

An buƙaci Sirika da ya gurfana a gaban kotu tare Fatima da Jalal Hamma da kuma Kamfanin Al-Duraq Investment Ltd, a gaban Mai Shari’a Sylvanus Oriji na Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja.

KU KUMA KARANTA: EFCC ta kama tsohon Ministan Jiragen Sama, Hadi Sirika

Ana tuhumar su ne da laifin yin amfani da mukamansu wajen karkatar da sama da Naira biliyan 2.7 daga ma’aikatar sufurin jiragan sama a zamanin shugabancin Hadi.

Karon farko ke nan da za a gurfanar da tsohon ministan a gaban kuliya.

Continue Reading

EFCC

Jerin sunayen tsofaffin gwamnonin da ake zargi da cin hanci ba daga wurinmu ya fito ba — EFCC

Published

on

Hukumar da ke Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Zagon-Ƙasa wato EFCC ta nesanta kanta daga wani jerin sunaye wanda ke yawo a wasu jaridu da kafafen sada zumunta da ke cewa tana bincikar wasu tsofaffin gwamnoni kan zargin rashawa.

A ranar Asabar ne wani labari ya rinƙa yawo kan cewa akwai tsofaffin gwamnoni 58 waɗanda hukumar ke bincika kan zargin almundahana ta kimanin naira tiriliyan 2.187 a cikin sama da shekara 25.

Sai dai a wata sanarwa da mai magana da yawun EFCC Dele Oyewale ya fitar a ranar Lahadi, ya bayyana rahotannin a matsayin na ƙarya.

Mista Oyewale ya bayyana cewa waɗanda suka ƙirƙiri jerin sunayen su kaɗai suka san manufar da suke son cimmawa.

KU KUMA KARANTA: Idan ban kama Bello ba, zan yi murabus daga kujerata – Shugaban EFCC

“Hukumar EFCC, tana ganin ya zama wajibi ta nesanta kanta daga wani rahoto da ke yawo a kafafen watsa labarai na cewa ta fitar da cikakken jerin sunayen tsofaffin gwamnonin da ake bincike kan zargin cin hanci da rashawa.

“Rahoton mai taken: “EFCC ta saki cikakken jerin sunayen tsofaffin gwamnoni 58 da suka wawure tiriliyan N2.187”, a wata kafar watsa labarai, karya ne kuma hukumar ba ta fitar da wannan jerin sunayen ba ko kuma tattaunawa kan binciken tsoffin gwamnoni da wata kafar yada labarai,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Sai dai a ƴan kwanakin da suka gabata hukumar ta EFCC ta yi ta bincikar wasu tsofaffin gwamnoni daga ciki har da tsohon gwamnan Kogi Yahaya Bello inda take zarginsa da cire dala miliyan 720 daga asusun jihar domin biyan kuɗin makarantar yaronsa.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like