No menu items!

Sample Page Title

Date:

Dokace ta bawa hukumar tace fina-finai damar tace kowanne nau’in Bidiyo – Isma’ila Afakallah

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Tsohon Shugaban Hukumar tace fina-finan da dab’i ta Jihar Kano, Isma’ila Na’abba Afakallah ya magantu, kan yadda ake Cece – kuce akan tsare – tsaren da Hukumar tace fina-finan keyi, karkashin jagorancin Abba El-Mustapha.

Wanda Afakallah yace hukumar nada damar yin hukunci ga duk wanda ya karya dokar hukumar, kuma hukumar nada hakki tayi doka akan dukkan bidiyon da aka fitar ko a wacce kafa ce.

KU KUMA KARANTA:Hukumar tace fina-finai ta kara soke lasisin wasu gidajen wasannin gala 8 tare da Haramta aikinsu na din-din-din a Jahar Kano

Afakallahu ya kuma ce, tabbas dole a yabawa tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, wanda shi ne ya kafa hukumar tace finafinai da dab’i ta Jihar Kano a zangon mulkinsa na farko (1999 – 2003), wacce har yanzu take taka rawa wajen tafiyar da harkokin nishadi don ganin ba’a sabawa addini ko al’ada ba.

Ya kuma ce, yaso ace a shugabancinsa aka yiwa dokar hukumar gyara, amma dukda haka yana goyon bayan matakan da hukumar ke dauka a yanzu, illa iyaka wasu ‘yan kura-kurai da yake fatan hukumar zata gyara.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...