No menu items!

Sample Page Title

Date:

Dangote ya yi ritaya a matsayin shugaban kamfanin sa

Daga Jameel Lawan Yakasai

Aliko Dangote ya yi ritaya daga matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwa na kamfanin sukari mai suna Dangote Sugar Refinery PLC, wanda hakan ya kawo karshen jagorancinsa na tsawon shekaru 20 a kamfanin.

Ritayar tasa za ta fara aiki daga ranar 16 ga Yuni, 2025, bisa wata sanarwa da sakataren kamfanin, Temitope Hassan, ya sanya wa hannu a ranar Laraba.

KU KUMA KARANTA: Kamfani na ne ke biyan haraji mafi yawa a Najeriya – Dangote

Dangote, wanda ya kasance shugaban kamfanin tun daga shekarar 2005, ana danganta masa gagarumar nasara wajen mayar da Dangote Sugar jagora a kasuwar masana’antar sukari a Najeriya, ta hanyar gudanar da manyan ayyukan fadada kamfani da kuma karfafa tsarin shugabanci mai nagarta.

Sanarwar ta bayyana cewa a lokacin shugabancinsa, kamfanin ya aiwatar da muhimman Ayyukan Haɓaka Noma a Jihohin Adamawa, Taraba da Nasarawa, don bunkasa samar da sukari a cikin gida da rage dogaro da shigo da kaya daga waje.

Sai dai an nada Arnold Ekpe, wanda ke matsayin Darakta Mai Zaman Kansa, a matsayin sabon shugaban kamfanin.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...