No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Kotun ƙoli ta tabbatar da nasarar Gwamna Ahmadu Fintiri na jihar Adamawa.
Kotun ƙolin ta kori ƙarar da ‘yar takarar kujerar gwamna ƙarƙashin jam’iyyar APC a babban zaɓen 2023, Sanata Aishatu Ɗahiru Binani, da ta shigar tana mai ƙalubalantar ayyana gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, a matsayin gwamnan jihar Adamawa.

Kotun ƙarƙashin jagorancin Mai shari’a John Okoro, ta tabbatar da cewa gwamna Ahmadu Umaru Fintiri shi ne halastaccen gwamna a jihar Adamawa.

Haka kuma Mai shari’a John Okoro ya bayyana cewa matakin da Kwamishinan hukumar Zaɓe na jihar (REC), Hudu Ari, ya ɗauka, wani aiki ne na rashin gaskiya da kuma aikata laifi.

KU KUMA KARANTA: NNPP ta yaba wa hukuncin da kotun ƙoli ta yanke kan zaɓen gwamnan Kano

Mai shari’a Okoro ya ci gaba da cewa, jami’i Mai sanar da sakamakon zaɓe ya kamata ya bayyana sakamakon zaɓe, domin a kaucewa hargitsi da ruɗani.

Ya bayyana cewa dokar zaɓe ta ba da alhakin wanda zai bayyana sakamakon zaɓe, kuma wannan iko ya rataya ne kawai ga jami’in da hukumar zaɓe INEC ta aiko Mai sanar da sakamakon zaɓe.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...