No menu items!

Sample Page Title

Date:

Da yawan ‘Yan Film sun talauce – Jarumi Tijjani Asase

Daga Jameel Lawan Yakasai

Jarumin masana’antar fim ta Kannywood, Tijjani Abdullahi Asase, ya yi kira ga gwamnatin jihar Kano da ta janye matakin hana saka tallukan magungunan gargajiya a finafinan Kannywood.

Gwamnatin jihar, ta hannun hukumar tace finafinai da ɗab’i ta jihar ce ta samar da hana saka tallan magungunan gargajiya a finafinan Hausa da kuma bakin tituna, inda ta ce ana amfani da kalamai na batsa da ka iya gurɓata tarbiyya.

KU KUMA KARANTA:Dokace ta bawa hukumar tace fina-finai damar tace kowanne nau’in Bidiyo – Isma’ila Afakallah

A wani faifen bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta, an hango Asase na kira ga gwamnatin da janye matakin duba da illar sa ga masana’antar Kannywood da dumbin masu aiki a karkashin ta.

A cewar Asase, masana’antar Kannywood ta talauce, inda masu shirya fim da jaruman duk su na cikin halin babu, kuma ta hanyar Sanya tallukan ne suke samu su rage asarar abinda suka kashe.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...