No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban Colombia Gustavo Petro ya ce za su yanke hulɗar jakadanci da Isra’ila kan yaƙin da take yi a Gaza.

Tuni da ma Petro yake caccakar Firaiministan Benjamin Netanyahu sannan ya yi kira ga Afirka ta Kudu ta saka shi a cikin ƙarar da ta kai Isra’ila a kotun duniya kan zarginta da kisan ƙare-dangi a Gaza.

KU KUMA KARANTA: Jami’ar Columbia ta yi barazanar korar masu zanga-zangar adawa da yaƙin Gaza

“A yanzu kuma a gabanku, gwamnatin canji da shugaban ƙasar jamhuriya suna sanar da cewa gobe za mu yanke hulɗar jakadanci da Isra’ila…saboda kasancewarta gwamnati da shugaban ƙasa masu kisan ƙare-dangi,” in ji Petro a yayin da yake jawabi ga dandazon jama’a a Bogota, don tunawa da Ranar Ma’aikata da kuma goyon bayan sauye-sauyen Petro kan walwala da tattalin arziki.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...