No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ammar Muhammad Rajab

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a jiya Lahadi ya naɗa ɗan majalisar Tarayya mai barin gado mai wakiltar ƙaramar hukumar Kano Municipal, Hon. Sha’aban Sharada a matsayin shugaban sabuwar Hukumar lura da Almajirai da waɗanda ba sa zuwa makaranta.

Da yake sanar da naɗin ga manema labarai, mai magana da yawun shugaban ƙasa, Mallam Garba Shehu, ya ce naɗin ya biyo bayan amincewar da shugaban ƙasa ya yi ne a kan ƙudirin dokar 2023 na bayar da ilimi ga almajirai da ƙananan yara da ba sa zuwa.

Sharaɗa dai ya yi Digirinsa na farko a ɓangaren aikin jarida a Jami’ar Bayero ta Kano, sannan kuma ya yi Digiri na biyu a fannin harkokin kasuwanci daga Jami’ar Chichester a Birtaniya.

Awanni kafin kammala wa’adin mulkinsa, Shugaba Muhammadu Buhari ya sanya hannu kan dokar kula da almajiranci.

KU KUMA KARANTA: Shugaba Buhari ya yi jawabin ban kwana ga ‘yan Najeriya

Majalisar wakilai ta Nijeriya ce ta fara amincewa da dokar kafin ta kai gaban shubaban, inda ya rattaɓa mata hannu.

Dokar dai na neman samar da tsarin ilimi mai kyau da bunkasa fasahar koyon sana’o’i da kuma rage talauci tsakanin almajirai a Nijeriya.

Har ila yau, dokar za ta kuma kyautata karatun tsangaya da rayuwar almajirai da sauran yaran da ke gara-ramba ba su zuwa makaranta.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...