No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya isa birnin Madina na ƙasar Saudiyya domin fara ziyarar aiki ta kwanaki takwas a ƙasar ta Gabas ta Tsakiya.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya bayar da rahoton cewa, jirgin shugaban ƙasar da ke jigilar shugaban Najeriya da wasu muƙarrabansa ya tashi daga filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe International Airport Abuja da ƙarfe 9:10 na safiyar ranar Litinin, ya sauka a filin jirgin saman Yarima Mohammed Bin Abdullaziz na Madina da misalin ƙarfe 17:00 na dare agogon gida.

KU KUMA KARANTA: NAHCON ta sanar da kuɗin aikin Hajjin bana

A lokacin da yake Madina, shugaban zai gudanar da salloli biyar na rana da kuma sallar tarawihi a masallacin Nabawi kafin ya tashi zuwa Makkah da Jeddah, da yammacin ranar Laraba, domin gudanar da aikin Umara.

Garba Shehu, mai magana da yawun shugaban ƙasar a ranar Litinin a wata sanarwa ya bayyana cewa ziyarar aiki ta bana daga 11 zuwa 19 ga watan Afrilu ita ce ziyarar Buhari ta ƙarshe a masarautar a matsayin shugaban ƙasa.

NAN ta ruwaito cewa shugaban ya kammala aikin Umrah ne a shekarar 2021.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...