No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani ɗan sanda da ke aiki a rundunar ‘yan sandan jihar Imo, Cosmas Ugwu, ya gamu da ajalinsa bayan budurwarsa ta harbe shi har lahira.

An kashe Ugwu ne a ranar Talata, 26 ga watan Disamba, bayan  budurwarsa mai shekaru 23, wacce aka bayyana sunanta da Amanda Uchechi Ugo, ‘yar asalin ƙaramar hukumar Ahiazu Mbaise ta jihar Imo ta harbe shi.

An tattaro daga majiya mai tushe cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 6:30 na yammacin ranar Disamba 26 a yankin Ezinihitte.

Marigayin ya yi faɗa da budurwar tasa a ɗakin da ke ofishin ‘yan sanda, kuma ana cikin rikicin ne sai yarinyar ta kai hannu ta ɗauki bindigar marigayin, ta ja bindigar ta harbe shi har sau uku.

KU KUMA KARANTA: Ɗan sanda ya kashe abokin aikinsa, ya harbe kansa

An ce jami’an da ke bakin aiki sun gudu ne bayan da suka ji ƙarar harbe-harbe har sau uku. 

Wata majiya ta ce a ranar Alhamis: “Lokacin da jami’an ‘yan sanda suka shiga ɗakin daga baya don ganin abin da ke faruwa, sai suka tarar da Kofur Ugwu a kwance a cikin jininsa.  

Yarinyar ta harbe shi har sau uku a ƙirjinsa da kuma hannun hagu. Nan take aka garzaya da shi Asibitin Evergreen da ke Ezinihitte, inda Likitan da ke bakin aiki ya tabbatar da mutuwarsa.”

“A zahiri babu wanda ya san abin da ya faru tsakanin su biyun, amma yadda yarinyar ta yi nasarar amfani da bindigar ‘yan sanda cikin nasara har yanzu abin mamaki ne ga mutane da yawa, wataƙila Ugwu ne ya koya mata.”

An ajiye gawar jami’in da aka kashe a ɗakin ajiyar gawa na Obizi yayin da ake ci gaba da bincike.

Wanda ake zargin tana hannun ‘yan sanda.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Imo, Henry Okoye, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce ‘yan sanda na yin duk abin da ya dace domin gano haƙiƙanin abin da ya faru.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...