Boko Haram a Yobe sun kashe mutane da dama da ƙona gidaje

2
180
Boko Haram a Yobe sun kashe mutane da dama da ƙona gidaje

Boko Haram a Yobe sun kashe mutane da dama da ƙona gidaje

Mayaƙan ƙungiyar Boko Haram sun hallaka mutane da dama, suka ƙona gidaje da kantuna tare da wawushe kayayyaki a ƙauyen Mafa da ke ƙaramar hukumar Tarmuwa ta Jihar Yobe.

Mayaƙa sama da 50 ɗauke da muggan makamai a kan babura ne suka far wa ƙauyen a yammacin ranar Lahadi.

Jami’in hulɗa da Jama’a na ’Yan Sanda a Jihar Yobe, DSP Dungus Abdulkarim, ne ya tabbatar da harin a Damaturu a safiyar Litinin.

DSP Dungus ya ce shaida wa Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) cewa “Zuwa yanzu ba mu tantance adadi rayukan da aka rasa ba, a harin da aka kai da misalin karfe 4 na ranar Lahadi.

“Wani daga ƙauyen Mafa ne ya kai rahoton harin ne a Babban Ofishin ’Yan Sanda na ƙaramar hukumar Tarmuwa.

KU KUMA KARANTA: Mun kashe ’yan boko haram 5, 44 sun miƙa wuya – Sojojin Najeriya

“Mayaƙan, ɗauke da manyan makamai har da RPG sun far wa gundumar Mafa, suka ƙona gidaje da kantuna.

“Sun kuma kashe mutane da dama, amma ba a kai ga tantance adadinsu ba,” in ji DSP Dungus.

Ya ƙara da cewa maharan sun kuma jefar da wasu takardu masu ɗauke da rubutun Larabci.

2 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here