Connect with us

Labarai

Bayan shekara 12 da rufe sansanin NYSC a Borno, an sake buɗe shi

Published

on

Hukumar Kula da Matasa Masu yi wa Ƙasa Hidima (NYSC) ta fara ba da horo ga matasa masu yi wa ƙasa hidima su 1,161 a sansanin horar da malamai na ATC da ke Jihar Borno.

Kimanin shekaru 12 ke nan sansanin ya shafe a rufe sakamakon ta’addancin Boko Haram.

Fara horarwar wanda aka shirya yi a ranar Juma’a mai zuwa a Maiduguri, zai gudana ne a sansanin mai ɗaukar mutane 3,000.

Shugaban hukumar a jihar, Mohammed Adamu, ya ce, “Sojoji, ’yan sanda da sauran jami’an tsaro sun tabbatar mana da tsaron jami’anmu, da jami’an wayar da kan jama’a da kuma jami’an hukumar da ke wannan sansani da aka gyara.”

Ya yi nuni da cewa, an dawo da shirin ne bayan shekaru 12 da Boko Haram ta fara ta’addanci a jihar kamar yadda aka ambata a baya.

KU KUMA KARANTA: Hukumar NYSC ta musanta tura membobin ƙungiyar zuwa jamhuriyar Nijar

Dangane da dabarun da sansanin yake da shi, ya ce: “Sansanin ATC na gwamnatin jihar da aka gyara yana tsakiyar ofisoshin hukumomin tsaro da ke kan titin filin jirgin saman ƙasa da ƙasa na Janar Muhammadu Buhari a Maiduguri.”

Don haka ya kawar da duk wata fargabar da iyaye da masu kula da su ke da ita ta kare lafiyar ’ya’yansu a lokacin da za su karɓi horo na mako uku.

Ya ƙara da cewa mazauna Maiduguri da suka haɗa da Shehun Borno, Alhaji Abubakar Ibn El-Kanemi, sun cika maƙil da farin ciki kan yadda za a dawo da horar da matasan a Jihar.

Da yake duba sansanin, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, Mohammed Yusuf, ya ce, “Maƙasudin ziyararmu ita ce duba yanayin tsaro a yankin, tare da sanin haƙiƙanin yadda aka tura jami’an tsaro.”

Don haka, Kwamishinan ya ba da tabbacin tura isassun jami’an ’yan sanda a wuraren shiga da fita sansanin, gami da muhimman wurare na tsaro.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Gwamnan Zamfara ya ba da umarnin a gyara sansanin NYSC na jihar | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Hukumar NYSC ta tabbatar da yin garkuwa da ɗalibai takwas a Zamfara | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like