Bai kamata ku tafi yajin aiki ana tsaka da tattaunawa ba, Gwamnatin tarayya ga ASUU
Daga Jameel Lawan Yakasai
Gwamnatin Taraiya (FG), ta bakin Ministan Ilimi, Dakta Maruf Tunji Alausa ta ce bai kamata ƙungiyar malaman jami’o’i ta ƙasa, ASUU, ta fara raba goron gaiyatar tafiya yakin aiki ba tunda ana tattaunawa da duk kungiyoyin da abin ya shafa.
Ya ce gwamnatin taraiya na iya bakin kokarin ta na gyaran makarantun gaba da sakandire a fadin Nijeriya.
KU KUMA KARANTA: Za mu shiga yajin aikin sai Baba-ta-gani – ASUU
Alausa ya roƙi ƙungiyoyin da ke shirin tafiya yajin aikin da su dakatar da shirin su tunda gwamnati na tattaunawa da su.









