No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga; Rabo Haladu.

AN ɗage shari’ar Mu’azu Magaji wanda aka fi sani da Ɗan Sarauniya zuwa Juma’a 4 ga watan Fabrairun 2022.

A cikin wata wasiƙa da Magatakardar Kotun Majistare da ke Nomansland da ke Kano Auwal Muhammad T/Wuzurci ya saka wa hannu, an ɗaga zaman ne saboda yanayi na staro.

Ya bayyana cewa a ranar 3 ga wata wadda ita ce asalin ranar da za a yi shari’ar Mu’azu Magaji, a ranar ne za a yi shari’ar Sheikh Abduljabar Nasiru Kabara kuma jami’an da za su kai Sheikh Abduljabar kotun da ake masa shari’a a Upper Shari’a Court da ke Ƙofar Kudu su ne dai jami’an da za su kai Mu’azu Magaji kotun da za a yi masa shari’a a Nomansland.

Hakan ya sa aka ɗage shari’ar Dan Sarauniya zuwa 4 ga watan Fabrairu da misalin 2:30 na yamma.

A makon da ya gabata ne ‘yan sanda a Abuja, suka kama Mu’azu Magaji wanda shi ne tsohon Kwamishinan Ayyuka na jihar Kano.

Sun kama shi ne bisa tuhume-tuhumen da Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje yake masa na ɓata masa suna da zaginsa da kuma zargin yin abubuwan da zai kawo taɓarɓarewar zaman lafiya.

admin
adminhttps://neptuneprimehausa.com
Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...