Connect with us

Labarai

An yi jana’izar mabiya Shi’a 6 da ‘yansanda suka kashe a Kaduna

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Jagoran ‘yan’uwa Musulmi a Kaduna da aka fi sani da ‘yan Shi’a ƙarƙashin jagorancin Shaikh Ibraheem Elzakzaky, Malam Aliyu Umar Tirmidhi ya shaida wa BBC cewa ‘yansanda sun auka musu tare da buɗe musu wuta ba tare da wani dalili ba, inda suka kashe mutum biyar da jikkata 25, a lokacin da suke gudanar da Muzaharar nuna goyon baya ga Falasɗinawa jiya Juma’a, a birnin Kaduna.

“Muna cikin muzaharar lami lafiya kawai sai muka ji ana harbe-harbe a bayanmu. Hakan ya sa muka yi addu’a muka ce kowa ya tafi gida. Ai kuwa kawai ‘yansanda suka ƙara buɗe wuta inda suka shahadantar da mutum biyar da jikkata 25.”

Mabiya Shaikh Zakzaky dai kan gudanar da muzaharar nuna goyon baya ga Al’ummar Falasɗinawa a duk juma’ar ƙarshen watan Ramadan.

KU KUMA KARANTA: An kama mutum 8 kan zargin kashe malami a Jami’ar Maiduguri

Malam Tirmidhi ya kuma ce a Zariya ma ‘yansandan sun harbe mutum ɗaya ya kuma ya yi shahada.

Dangane kuma da waɗanda aka kama, malam Tirmidhi ya ce yanzu haka suna haɗa alƙaluman domin tantance yawansu amma dai sun haƙƙaƙe cewa a yanzu mutum shida suna hannun ‘yansanda.

Rundunar ‘yansandan jihar Kaduna dai ta bakin mai magana da yawunta, ASP Mansir Hassan, ta ce “mutanen sun fito ɗauke da makamai kuma suka far wa al’ummar gari wannan ya sa muka tarwatsa su sannan mun kama wasu za mu gurfanar da su a kotu.”

To sai dai malam Tirmidhi ya ce wannan maganar ba gaskiya ba ne.

“Mu da muka fito mata da maza sannan ƙanana da manyanmu wato ƙwanmu da ƙwarƙwata yaya za a yi mu ɗauki makami har mu fara far wa jama’a? Ai hankali ba zai ɗauka ba.”

Tuni dai har an yi jana’izar waɗanda ‘yansandan suka kashe kamar yadda addinin musulunci ya tanadar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like