No menu items!

Sample Page Title

Date:

’Yan bindiga sun yi garkuwa da wasu matan aure takwas a wata gona a ƙaramar hukumar Kuje da ke yankin Babban Birnin Tarayya.

An yi awon gaba da matan auren ne kwanaki kaɗan bayan ’yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifin mataimakin Shugaban ƙaramar hukumar Kwali da wasu mutum shida daga ƙauyen Yewuti.

Wani mazaunin ƙauyen Gwombe da ke masarautar Gwargwada Usman Yakubu, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 5 na yammacin ranar Litinin.

Ya ce matan auren suna tsaka da shuka iri ne ’yan ta’adda ɗauke da bindigogi ƙirar AK-47 suka yi musu kawanya suka yi awon gaba da su zuwa inda ba a sani ba.

Wani basarake daga wani ƙauye a masarautar, wanda ya buƙaci a sakaya sunansa, ya tabbatar da sace matan.

KU KUMA KARANTA: Yadda yaro ɗan shekara 9 ya yi garkuwa da ƴar shekara 5 a jihar Bauchi

“Hakika, huɗu daga cikin matan ’yan gida ɗaya ne,” a cewarsa,

Ya ci gaba da cewa, “ina zargin waɗannan ’yan bindiga da suka yi garkuwa da matan na daga cikin waɗanda suka tsere daga ƙauyen Kabbi da ke makwabtaka da su da suke yawo a cikin daji bayan ’yan bangar Miyetti Allah suka kashe wasu daga cikinsu a ƙarshen mako.”

Babu wani martani daga kakakin rundunar ’yan sandan babban birnin tarayya, SP Adeh Josephine, kan lamarin.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...