Connect with us

Al'ajabi

An yankewa mahaifiya hukuncin ɗaurin rai da rai, bisa laifin kashe ‘yarta

Published

on

An yankewa wata uwa a Houston hukuncin ɗaurin rai da rai a gidan yari saboda ta yi ma ‘yarta, ‘yar wata huɗu dukan tsiya ta mutu har Lahira, a cewar lauyan gundumar Harris Kim Ogg.

Tradezsha Trenay Bibbs, mai shekaru 29, an same ta da laifin kisan kai saboda mutuwar ɗiyarta mai watanni 4, Brielle Robinson, a ranar 16 ga Afrilu, 2016. A baya dai an yanke wa Bibbs hukuncin kisa a gaban shari’a, amma daga baya aka yanke hukuncin ya juya ɗaurin rai da rai.

A cikin shekarar 2016, an ƙira hukumomi zuwa ‘Red Carpet Inn’ dake kan hanyar teku, inda suka sami Bibbs a cikin ɗaki tare da Brielle. A cewar takardun kotun, Bibbs ta shaida wa jami’an cewa ta ji ‘yarta na kuka, sannan ta ɗauke ta da hannu, lamarin da ya sa ta faɗi daga kan gadon zuwa ƙasa.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun kashe ‘yan bindiga biyu a Zamfara

Sai Bibbs ta yi ta bugun ’yarta a fuska, kirji, haƙarƙarinta, da ƙafafuwa har sai da yarinyar ta daina kuka. Daga baya an kai Brielle zuwa Asibitin Yara na Texas, inda likitoci suka gano cewa ta sami karaya da yawa da ciwon kai. Da farko Bibbs ta gaya wa hukumomi cewa Brielle ta faɗo daga kujerar motar ta kan siminti, amma daga baya ta yarda cewa ta yi wannan ɗanyan aiki.

Ta shaida wa ’yan sanda cewa bayan ta shiga otal ɗin da jaririyar, bayan ‘yan sa’o’i kaɗan sai ta jefar da ita a kan katifa ta yi mata naushi a fuska, haƙarƙarinta, da ƙirji har sai da ta daina kuka.

Bibbs ta kira 911 da zarar jaririn ya daina numfashi. Mataimakin Lauyan Gundumar Keaton Forcht ya ce Bibbs ta kashe ɗiyarta saboda mahaifin jaririn baya son dangantaka da Bibbs. A cikin shari’ar da aka shafe mako guda ana yi, masu shari’a sun ji shaidar cewa likitocin ɗakin gaggawa sun ce Bibbs ba ta sha’awar kula da lafiyar jaririyar ko sakamakon mummunan rauni da ta yi.

“Bibbs ta cancanci hukuncin ɗaurin rai da rai saboda abin da ta yi wa ‘yarta,” in ji Forcht. “Ta buge ta sau da yawa kuma da alama ta damu da mutuwar ‘yarta kamar yadda ta damu da rayuwar ‘yarta.”

Ogg ya ce “Ofishin mu yana tsayawa ne ga duk waɗanda abin ya shafa, amma jariraine ne mafi yawan waɗanda abin ya shafa,” in ji Ogg. “Mun yi imanin cewa hukuncin ɗaurin rai da rai ya dace da wannan kisan gilla, kuma Alƙalai na gundumar Harris sun amince.”

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Masu ƙwacen waya sun yi yunƙurin hallaka ɗan Jarida a Kano | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Masu ƙwacen waya sun yi yunƙurin hallaka ɗan Jarida a Kano - LEGEND FM DAURA

  3. Pingback: Fusatattun matasa sun kashe mutum 1, sun ƙona gidaje 64 da babura 3 a Bauchi | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Al'ajabi

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Published

on

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta yayin da mutane ke Sallar Asuba ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Gadan da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar ta Kano, da misalin karfe 5:20 lokacin da ake sallah, a cewar sanarwa ‘yan sanda.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa da TRT Afrika Hausa faruwar lamarin da kama mutumin da ake zargi, sai dai ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Abdullahi Kiyawa ya ce bincike ya nuna cewa mutumin da ake zargi da cinna wutar Shafi’u Abubakar mai kimanin shekaru 38 ya jefa wata roba ne ɗauke da fetur cikin masallacin, sannan ya cinna wuta.

KU KUMA KARANTA: Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus

Kakakin ‘yan sandan ya ce mutum 24 ne suka ƙone a masallacin, da suka haɗar da manya 20, yara huɗu.

An garzaya da duka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti don ba su kulawa, amma babu wanda ya mutu a haɗarin, a cewar sanarwar ‘yan sandan.

Continue Reading

Al'ajabi

An tsinci gawar wata ɗaliba a cikin ɗaki a Kano

Published

on

An tsinci gawar wata ɗaliba mai suna Aisha Yahaya ta Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, a wani gida da ke wajen jami’ar.

Aisha, ɗaliba ce da ke matakin karatu na uku wato ‘level 300’ a sashen nazarin Kimiyya da Fasahar Abinci na jami’ar wadda aka tsinci gawarta bayan ta koma ɗakinta.

An ce ɗalibar ta rubuta jarrabawarta ta farko a zangon karatun na farko da ake yi a jami’ar.

Wasu daga cikin abokan karatunta sun danganta mutuwarta da shiga cikin matsi da damuwa a dalilin karatu da kuma zana jarrabawar.

A cikin wasiƙar ta’aziyyar, hukumar jami’ar ta bayyana matuƙar baƙin cikinta dangane da rasuwar Aisha Yahaya.

KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar wani mutum a kan titi a Kano

Sanarwar ta ce, “Aisha ɗaliba ce mai hazaƙa wadda ta rasu a dalilin bugun zuciya. Za a riƙa tunawa da ita a kan sha’awarta na karatu da jajircewarta kan harkokin karatunta.”

Jami’ar ta ƙara da cewa, ba a iya gano wata da ke tattare da ita ba gabanin mutuwarta saboda ba ta nuna alamun rashin lafiya ko fama da wata cuta ba.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like