Connect with us

Laifi

An tsare ɓarayi 2 kan satar buhun zoɓo 10 a Jigawa

Published

on

Jami’an Hukumar Sibil Difens a Jihar Jigawa, sun cafke wasu mutum biyu da ake zargi da satar buhun zoɓo guda 10 a jihar.

Kakakin rundunar, ASC Badruddeen Tijjani Mahmud, ya ce an kama waɗanda ake zargin ne a ƙaramar hukumar Hadeja.

Ya ce, an kama su ne a ranar Lahadi 21 ga watan Janairu, 2024 da misalin ƙarfe 8:30 na safe a unguwar Gawuna da ke Hadeja.

A cewarsa an cafke su ɗauke da buhu 10 na zoɓo wanda ake zargin na sata ne.

KU KUMA KARANTA: An kama wasu manyan ɓarayin wayar salula da POS guda huɗu

Mahmud, ya ce bincikensu ya nuna cewa waɗanda ake zargin sun haɗa baki tare da fasa shagon wani Alhaji Yusuf Idris da ke Gawuna a ƙaramar hukumar Hadeja.

Ya ce sun yi awon gaba da buhu 10 na zoɓo.

Amma kakakin ya ce, an ƙwato buhun zoɓon gaba ɗaya, wanda darajarsa ta kai baira N362,250.

Kazalika, ya ce an kama ɓarayin da wasu ƙarafa da adduna da suke amfani da su wajen fasa shagunan al’umma a yankin.

Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Click to comment

Leave a Reply

Laifi

‘Yan bindiga a Kaduna sun kashe wani likita da sace mutane 8

Published

on

'Yan bindiga a Kaduna sun kashe wani likita da sace mutane 8

‘Yan bindiga a Kaduna sun kashe wani likita da sace mutane 8

Daga Ali Sanni Larabawa

‘Yan bindiga sun kashe wani likita tare da sace wasu mutane 8 a garin Kwassam da ke ƙaramar hukumar Kauru a jihar Kaduna.

‘Yan bindigar sun kashe wani likita tare da yin garkuwa da wasu mutane 8 a garin Kwassam da ke ƙaramar hukumar Kauru a jihar Kaduna.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, ɗan majalisar tarayya na Mazabar Kauru, Hon. Zakari Ahmad Chawai, ya ce ana yawan samun hare-haren akai akai a mazaɓun Kwassam da Dawaki dake ƙaramar hukumar ta Kauru.

“Kwanaki huɗu da suka wuce ’yan bindigar sun kai hari a wata unguwa dake cikin mazaɓar Dawaki inda suka sace wasu mazauna yankin, kuma jiya sun sake kai hari a unguwar Kwassam,” in ji shi.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga a Binuwai sun ƙona gidaje 23

Yace, masu garkuwa da mutanen sun kashe mutun ɗaya, sun sace mutane 8 kuma sun tafi da wasu kayayyakin mutane da ba’a tantance adadinsu ba.

Hon. Chawai ya yi ƙira ga jami’an tsaro da su ƙara ƙaimi wajen magance hare-haren dake yawan faruwa a yankunan Kwassam da Dawaki.

Rahotanni sun nuna cewa mazauna yankin suna ci gaba da gudanar da ayyukansu na yau da kullum kamar yadda suka saba bayan lafawar abin.

Sai dai har yanzu babu wani bayani daga masu garkuwar kan batun kuɗin fansa, kamar yadda wani mazaunin Kwassam ya shaidawa manema labarai.

Continue Reading

Labarai

‘Yan bindiga a Binuwai sun ƙona gidaje 23

Published

on

'Yan bindiga a Binuwai sun ƙona gidaje 23

‘Yan bindiga a Binuwai sun ƙona gidaje 23

Daga Ali Sanni

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin makiyaya ne sun ƙona gidaje 23 a yankin Egwuma da ke ƙaramar hukumar Agatu dake jihar Binuwai.

Mazauna yankin sun bayyana cewa mutane da dama sun tsallake rijiya da baya a harin wasu kuma da raunukan harbin bindiga.

Shugaban ƙaramar hukumar Gari, Philip Ebenyakwu, ya shaida wa manema labarai a Makurɗi, babban birnin jihar, cewa mutane uku ne suka tsira da raunukan harbi.

KU KUMA KARANTA: Mayaƙan ‘Boko Haram’ a Borno sun kashe ɗan sanda da ƙona motocin sintiri

Ya bayyana cewa ba a samu asarar rai ba, kuma waɗanda aka ji wa raunukan suna samun kulawa a asibiti.

Ya ce, “Makiyaya ɗauke da makamai daga jihar Kogi suna yawan kai hare-hare a Agatu ta yamma.

“Yankin da aka kai wa hari yana iyaka da jahar Kogi, kuma yana yawan fuskantar barazana.

“Ranar lahadi makiyayan suka kai hari a yankin Egwuma, inda suka ƙona gidaje 23 suka sace babura biyu.”

Duk da haka, Ebenyakwu, ya yaba wa jami’an tsaron da aka tura yankin.

Ya bayyana cewa a ranar Asabar wani sojan ruwa ya ƙwace jirgin ruwa da ’yan bindiga ke shigowa a kai daga jihar Nasarawa.

Wakilinmu yayi ƙokarin tattaunawa da kakakin ‘yan sandar jihar ta Binuwai, SP Catherine Anene, amma hakan baiyuba.

Continue Reading

Labarai

’Yan bindiga a Taraba sun harbe matafiya 7 a hanya

Published

on

’Yan bindiga a Taraba sun harbe matafiya 7 a hanya

’Yan bindiga a Taraba sun harbe matafiya 7 a hanya

Mahara sun harbe matafiya bakwai har lahira a safiyar Litinin a kan babbar hanyar Takum zuwa Wukari da ke Jihar Taraba.

Mahara sun harbe wasu matafiya guda bakwai har lahira a safiyar Litinin a kan babbar hanyar Takum zuwa Wukari da ke jihar Taraba.

Kisan gilla da aka yi wa matafiyan da direban motarsu ya haifar da zaman ɗar-ɗar a yankin Takum.

Shaidu sun bayyana wa wakilinmu cewa ɗauƙacin matafiyan waɗanda ’yan garin ne, suna hanyarsu ta zuwa garin Sa’ayi da ke Jihar Binuwai ne lokacin da harin ya rutsa da su a tsakanin garin Chanchangin da garin Wukari.

Wani shaida ya ce maharan sun buɗe wa motar wuta ne suka kashe duk mutanen da ke cikinta, nan take, amma ba su ɗauki komai ba a cikinta.

KU KUMA KARANTA: Mutane 9 ne suka mutu a rikicin ‘yan bindiga a Libya

Ya yi zargin maharan na daga cikin ’yan ta’addan da suka addabi dazukan da ke tsakanin Jihar Binuwai da Jihar Taraba.

A bisa wannan hanya ce dai aka kashe basaraken garin Chanchangi da babban ɗansa a watan Yuli.

Hanyar ta zamo tarkon mutuwa saboda ayyukan ’yan ta’adda da ke yin fashi da kuma garkuwa da matafiya domin karɓar kuɗin fansa a cikin dare da yini.

An tuntuɓi kakakin ’yan sandan jihar Taraba, DSP kwach,  game da harin na safiyar Litinin, amma jami’in ya ce masa sa zai bincika.

Continue Reading

You May Like