No menu items!

Sample Page Title

Date:

A ranar Asabar, 21 ga watan Oktoba, jami’an tsaro na haɗin gwiwa da suka haɗa da jami’an ‘yan sandan Najeriya, da na sojojin Najeriya da dai sauransu, sun kama wasu mutane huɗu da ake zargi da hannu a fashin bankin Benuwe da ya yi sanadin mutuwar wasu jami’an ‘yan sanda a kan hanyar Otukpo- Taraku a jihar Binuwai.

Wata majiyar ‘yan sanda ta shaida wa jaridar Punch cewa; “Jami’an tsaro na haɗin gwiwa sun kama wasu ‘yan fashi da makami huɗu a kan hanyar Otukpo-Taraku, jihar Benuwe a ranar Asabar. 

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kai hari kan bankuna a Benuwe, sun kashe mutane takwas

‘Yan fashin na daga cikin ‘yan fashi da makami da suka kai hari a bankuna da ofishin ‘yan sanda a Otukpo a jihar Binuwai.”

Da aka tuntuɓi jami’ar hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Binuwai, SP Catherine Anene, ta buƙaci manema labarai da su jira kammala binciken da rundunar ta ke gudanar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...