Connect with us

Kiwon Lafiya

An haifi jariri na farko ta hanyar IVF a Asibitin koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello Zariya

Published

on

Sashin Magungunan Haihuwa na Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello (ABUTH) da ke Zariya, an shirya shi don samar da In-Vitro Fertilisation, (IVF), wato a ɗebo maniyyin namiji a zuba a ƙwan mace kuma ta samu ciki ta haihu.

Farfesa Adebiyi Adesiyun na sashen kula da magungunan haihuwa na ƙungiyar ‘IVF Project’, ya bayyana haka a wata hira da ya yi da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ranar Alhamis a Zariya.

Mista Adesiyun ya bayyana hakan ne a kan ci gaban da ABUTH ta samu, a matsayin asibitin gwamnati na farko a yankin Arewa maso Yamma da ya samu haihuwa wanda aka yi amfani ta hanyar IVF.

Ya ƙara da cewa an haifi jariri namiji da ƙarfe 10:53 na safiyar ranar 16 ga watan Mayu mai nauyin kilogiram uku (3kg). Duk da an fuskanci ƙalubale iri-iri amma an yi nasara.

KU KUMA KARANTA: Yadda mace mai ciki ta mutu a asibitin Kano sakamakon rashin takardun kuɗi

“Duk da haka, idan aka yi la’akari da waɗannan ƙalubalen ƙungiyar ta tuntuɓi babban Daraktan Likitoci, Farfesa Hamid Umdagas, da shawarar yin haɗin gwiwa da wani asibiti mai zaman kansa, don ba da wannan magani ga jama’a,” in ji shi.

Ya ce hukumar ce ta wajabta kuma an yi wannan aikin na farko ne tare da haɗin gwiwar wata cibiyar kula da haihuwa a Kaduna.

A cewarsa, haɗin gwiwar ya ta’allaƙa ne kan amfani da ɗakin gwaje-gwajen haihuwa na cibiyar haihuwa mai zaman kanta da ke Kaduna, wajen tattara ƙwan mata da maniyyin maza domin samun ciki a haihu.

Ya bayyana cewa an yi sauran abubuwan da suka shafi jinya da kula da marasa lafiya a ABUTH. “Mun fara ba da daɗewa ba, mun yi keke biyu kuma muna da wasu marasa lafiya da ke jiran karɓar magani.

“Muna da asibitoci a ranar Litinin, idan kun zo za ku iya ganin adadin marasa lafiya da ke son a musu hakan,” “in ji shi.

Ya ce manufar sashen ita ce a samu cikakkiyar cibiyar haihuwa inda kuɗin hidimar zai yi sauƙi sosai.

Shi ma da yake jawabi, wani memba na ƙungiyar, Farfesa Solomon Avidime, ya ce sashin kula da lafiyar haihuwa na asibitin yana da isasshen ƙarfin da zai iya biyan buƙatun mutanen da suke son ɗaukar ciki.

Mista Avidime ya ce babban abin da ke damun su shi ne samar da kuɗaɗe, musamman don ginawa da samar da kayan aikin da ake shirin samarwa a cibiyar haihuwa a ABUTH.

Ya bayyana cewa akwai ƙalubale wajen samun tallafin daga ƙasashen waje domin ƙasashen da suka ci gaba na ganin cewa yawan jama’a shi ne matsalar Najeriya ba ƙarancin al’umma ba, wanda hakan zai sa a yi wahala a samu tallafin da ƙasashen waje ke yi wa waɗannan ayyuka.

“Muna buƙatar gwamnati ta fahimci cewa akwai gungun mata da maza, waɗanda ke shan wahala saboda ba su da ‘ya’yan nasu.

“Wannan rukunin mutane ne kawai za su iya samun yara ta hanyar fasahar IVF, don haka ya kamata gwamnati ta kawo musu agaji ta samar musu da ayyukan yi.

Ya ce mahukuntan ABUTH sun taimaka; tana ƙoƙarin kafa cikakkiyar cibiya ta haihuwa ƙarƙashin haɗin gwiwar jama’a masu zaman kansu, don samar da ayyukan da ake samu da sauƙi.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Likitocin ƙasar Saudiyya sun yi nasarar raba tagwaye ‘yan Najeriya da suka haɗe | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Likitocin ƙasar Saudiyya sun yi nasarar raba tagwaye ‘yan Najeriya da suka haɗe - LEGEND FM DAURA

  3. Pingback: Gwamnatin Najeriya ta shigar da naƙasassu 500 shiga tsarin NHIS | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kiwon Lafiya

Gwamnatin tarayya ta hana amfani da sirinjin allura na ƙasashen waje a manyan asibitoci ƙasar

Published

on

Gwamnatin tarayya ta umurci dukkan shugabannin manyan asibitocin gwamnatin tarayya da su sayi allura da su riƙa amfani da allura da da ake ƙera su a gida kuma hukumar NAFDAC ta amince da su.

Sabuwar umarnin na ƙunshe ne a cikin wata takardar ga dukkan shugabannin asibitoci mai ɗauke da sa hannun ƙaramin ministan lafiya, Dakta Tunji Alausa, a yau Juma’a.

Ministan ya ce an ba da wannan umarnin ne domin bunƙasa samar da kayayyakin da ake ƙera wa a cikin gida da kuma kare masana’antun ƙasar daga kwararar kayayyakin ƙasashen waje.

Sanarwar ta kuma umarci hukumar ta NAFDAC ta dakatar da bayar da lasisin shigo da allura da sirinji da aka ƙera daga ƙasashen waje.

Alausa ya ce ɓangaren lafiya ya gano masana’antar har haɗa magunguna ta cikin gida da ke samar da allura da sirinji waɗanda ke cikin matsala matuƙa saboda wannan mummunar harkar.

Ya kuma ce daga cikin kamfanonin har haɗa magunguna guda tara na cikin gida da suke samar da allura da sirinji shekaru takwas da suka gabata, shida sun rufe saboda zubar da kayayyakin da ba su da inganci a kasuwa.

KU KUMA KARANTA:NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

“Shugaban ƙasa ya ba da umarnin cewa dole ne a daina wannan. Dukkanmu mun amince da ɗaukar matakan da suka dace don magance wannan mummunan yanayi cikin gaggawa.

“A bisa haka, hukumar ta NAFDAC ta dakatar da bayar da lasisin shigo da allura da sirinji da aka ƙera daga ƙasashen waje.

“Haka kuma shi ne a soke jerin sunayen kamfanonin da ke da hannu wajen shigo da waɗannan kayayyakin da ke ci gaba,” in ji shi

Continue Reading

Kiwon Lafiya

Amfanin ‘Dental floss’ a haƙora don tsaftace baki

Published

on

Daga Aisha Musa Auyo

Dental floss dai wani zare ne siriri na roba da ake sawa a tsakanin haƙora don cire abincin da ya maƙale a wurin. Wannan abinci da ke maƙale a tsakanin haƙora, brush ba ya fitar da shi. Shi ne yake taruwa ya zama ‘plaque’. Shi plaque ɗin wannan abincin da ya maƙale ne yake taruwa sai ya zama abincin bacteria.

Wannan dattin yana sa baki wari, yana sa haƙora su canza kala. Yana sa haƙora su yi ta ciwo wataran ma har sai an cire haƙorin, domin wannan bacteriar da ke ci daga gareshi tana kashe haƙori.

To shi wannan zaren yana zuwa a nau’i daban-daban, an yi shi ne siriri yadda ze iya shiga tsakanin haƙora yana fito da duk abin da ya maƙale ba tare da an wahala ba ko an ji zafi. Wani yakan zo da ƙamshin minti, vanilla, da sauransu, wani kuma kawai zaren ne babu ƙamshi.

Mafi yawancin ciwon haƙori ko warin baki wannan maƙallen abincin ke kawo shi. Idan mutum ya je Asibitin haƙori, akan yi masa wannan sakace tsakanin duk haƙoransa duka. Wato duk ranar da kuka fara flossing zai sha mamakin abin da zai fito tsakanin haƙoranku.

KU KUMA KARANTA: Sama da mutane miliyan 73 ne ke fama cutar ruɓewar haƙora a Filipin

Wato abin ya bani mamaki da na tambayi mutane ko suna flossing na ga da yawansu ba su ma san mene ne shi ba. Kamata ya yi flossing ya zama normal kamar brush. A ƙa’ida akan so mutum ya yi wannan sakacen tsakanin haƙoran kamar sau biyu a rana, yadda yake brush, amma mutum zai iya yin fiye da haka. In da hali duk lokacin da mutum ya ci abinci ya kamata ya yi flossing.

Akwai mouth wash da kan taimaka wajen fitar da waɗannan maƙallalun abincin, yayin da aka kurkure baki da shi na mintuna. Haka zalika, kurkure baki da ruwan kananfari ma na taimakawa wajen fiddasu. Amma babu abin da ya kai saka wannan zare a tsakanin haƙora ɗaya bayan ɗaya fitar da wannan abu da ke maƙalewa a tsakanin haƙoran.

Dan Allah a guji tsinken sakace, ba ɗaya yake da floss ba. Shi tsinken yana da kauri yana sa a samu rami tsakanin haƙoran da ake yawan sakace wa. Sannan katako ne yakan karye ma, kuma yakan jima mutum rauni.

A taƙaice, yin floss na ƙara wa mutum lafiyar haƙora, kyan haƙora, numfashi mai tsafta, da kuma jin daɗi wajen mua’amala da jamaa. Yin floss na raba mutum da ciwon haƙori, da kuma dauɗar haƙora. Floss na da sauƙin kuɗi sosai, ana iya samunsa a manyan shaguna, ko asbitin haƙori, har ma da wurin masu sayar da robobin abincin biki, domin ana sa shi a cikin packs ɗin abinci.

Dan Allah ka da mu yi wasa da yin floss. Akwai Hadisin da Annabi Muhammad (SAW) ya ce, ba dan ka da ya takurawa al’ummarsa ba, da ya mayar da yin aswaki kafin yin kowacce sallah ya zama wajibi. Wannan yana nuna mana tsantsar amfanin tsaftar baki ko a addini ma.

Continue Reading

Kiwon Lafiya

Cutar sanƙarau ta kashe mutum 85 a Yobe

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Gwamnatin jihar Yobe ta ce cutar sanƙarau ta kashe mutum 85 tsakanin Janairu da Afrilu sakamakon ɓarkewar cutar a jihar.

Kwamishinan lafiya na jihar, Dakta Muhammad Lawan Gana ne ya tabbatar da hakan a wani taron manema labarai a birnin Damaturu.

Ya ƙaryata rahotannin da ake yaɗawa a shafukan sada zumunta da ke cewa cutar ta yi ajalin sama da yara 200 cikin mako biyu inda ya ce haƙiƙanin adadin shi ne 85.

Ya kuma ce fiye da marasa lafiya 2,510 da suka kamu da cutar a jihar sun samu sauƙi kuma an sallame su daga asibiti.

KU KUMA KARANTA: Gwamnati ta musanta mutuwar mutum 200 sanadiyar baƙuwar cuta a Yobe

Dakta Gana ya kuma ce an tura jami’an lafiya na sa kai sama da 200 zuwa sassan ƙananan hukumomin Potiskum da Fika a wani ɓangare na ƙoƙarin da ma’aikatar take na daƙile cutar.

Ya ce ma’aikatan lafiya sun bi gida-gida domin ganowa tare da tura mutanen da ke da cutar asibiti.

Yankunan arewacin Najeriya na fama da matsanancin zafi a tsukin nan, yanayin da ke haddasa cutar ta sanƙarau.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like