No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani magidanci mai shekaru 40, Ayodeji Abayomi, ya gurfana a ranar Alhamis a wata kotun Majistire ta Iyaganku, Ibadan bisa zarginsa da cizon leɓan matarsa.

‘Yan sanda sun tuhumi Mista Abayomi, wanda ba a ba da adireshin gidansa da laifin cin zarafi. Ɗan sanda mai shigar da ƙara, Philip Amusan, ya shaida wa kotun cewa wanda ake tuhumar ya aikata laifin ne a ranar 24 ga watan Afrilu da misalin ƙarfe 7 na safe a unguwar Abebi, Ibadan.

KU KUMA KARANTA: An maka magini a kotu, bisa laifin satar buhunan siminti 50

Mista Amusan ya yi zargin cewa Abayomi ya cizi leɓan matarsa ​​Lilian na ƙasa. Ya ce laifin ya ci karo da tanadin sashe na 335 na dokokin aikata laifuka na jihar Oyo, 2000. Mista Abayomi, ya ƙi amsa laifin da ake tuhumarsa da shi.

Alƙalin kotun, O. A. Akande, ya shigar da ƙarar wanda ake tuhumar da bayar da belinsa a kan kuɗi naira 50,000 tare da mutane biyu masu tsaya masa.

Ta ɗage sauraron ƙarar har sai ranar 5 ga watan Yuni domin sauraren ƙarar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...