No menu items!

Sample Page Title

Date:

An tuhumi Hafsa Surajo da zargin laifin yunkurin kashe kai da kisan kai wanda ya saɓawa sashi na 281 da 221 na kundin laifuffukan na ƙasa a gaban kotun majastiri mai lamba 37 da ke yan kaba.

Neptune Hausa ta rawaito cewa, Hafsah Surajo da take hannun ‘yan Sanda tace tayi yunƙurin yanka kanta da wuka a gidanta dake unguwa uku inda Na’fi’u wanda yaron gidanta yayi ƙoƙarin hanata inda ta cakamasa a kirji da sassan jikinsa.

Bayan karanta mata tuhumar ta amsa yunƙurin kashe kanta amma ta musanta kashe Na’fi’u.

Mai gabatar da ƙara barista Lamido Abba Soron Dinkin yayi roƙo ƙarƙashin sashi na 295 ACJL da ajiye ta a gidan gyaran halin da tarbiyya kafin a sami shawarwari daga ma’aikatar Shari’a tun da kotun bata da hurumi.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sandan jihar Kano sun kama matar da ake zargi da kashe wani mutum (Bidiyo)

Mai Shari’a Hadiza Abdurrahaman ta aike da ita zuwa gidan gyaran halin da tarbiyya sai ranar 1 ga watan 2 na shekara mai kamawa 2024.

Barista Rabi’u Sidi shine lauyan dake kare Hafsan a gaban Kotun.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...