No menu items!

Sample Page Title

Date:

Fadar White House ta ce ba a gabatar wa Amurka da wani shirin Isra’ila na kare lafiyar fararen hula a Gaza ba idan har sojoji suka kutsa Rafah don fara kai hare-hare.

“Ba a gabatar mana da wani tsari ko ɗaya ba. Ba zan iya magana ga yawun Isra’ilawa ba ko kuma matakin da shirinsu ya kai ko kuma yadda hakan zai kasance ba,” in ji kakakin Kwamitin Tsaron Amurka John Kirby a wani taron manema labarai.

Isra’ila na shirin faɗaɗa hare-hare ta kasa zuwa Rafah, birnin da ke kudancin Gaza da ke kan iyaka da Masar, kuma mahaifar Falasdinawa miliyan ɗaya da dubu 400 ne, a daidai lokacin da kasashen duniya ke gargadin illar da hakan zai haifar.

KU KUMA KARANTA: Falasɗinu ta buƙaci Isra’ila ta biya kuɗin sake gina Gaza

Kirby ya yi nuni da cewa, Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce ya ɗora wa janar-janar ɗinsa aikin samar da wani shiri.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...